Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP
Published: December 7, 2025 at 10:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar, ya yi jawabi ga sojojin rundunar Birget na 25 na Sojin Najeriya, inda ya bayyana goyon bayan jihar ga yakin da suke yi da ‘yan ta’addan Boko Haram/ISWAP.

Gwamnan, wanda ke jawabi a sansanin sojoji a Damboa, ya tausaya wa jami’an da sojoji, yana mai godiya ga dimbin sadaukarwar da suka yi da kuma kokarin da suke yi a kullum.

Ya yaba wa abin da ya bayyana a matsayin “Namijin kokarinsu da kuma sadaukarwar su” a yakin da ake yi don kare Jihar Borno da kuma kare fararen hula daga barazanar Boko Haram da kuma Islamic State West Africa Province (ISWAP).

Zulum ya ce, “A madadin gwamnati da mutanen jihar Borno, Mun zo Damboa don yi muku jaje kan koma bayan da ya yi sanadiyyar mutuwar wasu daga cikin abokan aikin ku.

Yace Wannan lamari ne mai ban takaici, kuma ina so in mika ta’aziyyata gare ku da iyalan dukkan jami’ai da ma’aikatan wannan runduna da suka rasa rayukansu yayin da suke gudanar da ayyukansu tare da addu’ar Allah yabawa wadanda suka ji rauni a fagen daga lafiya da wuri-wuri.

Ga wadanda daga cikinku wadanda har yanzu suna raye kuma suna cikin koshin lafiya, muna addu’ar Allah ya kare ku, ya ba ku hangen nesa da karfin aiwatar da ayyukanku yadda ya kamata, sannan muna yabawa da goyon bayan ku kuma muna so mu yaba muku.

Gwamnan ya samu tarba daga Kwamandan Rundunar Sojoji ta 25, Brigadier Janar Igwe Patrick Omokeh.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na rangadin Zulum ga al’ummomi a kudancin Borno.

A farkon yinin ranar, gwamnan ya gana da iyalai dake cikin alhini a Chibok, inda ya yi musu ta’aziyya game da asarar rayuka da dukiyoyi, ya kuma yi ta’aziyya da kuma jaje ga waɗanda suka rasa kadarori.

A lokacin taron a Chibok, gwamnan ya sanar da matakai na musamman don kare rayuka da dukiyoyi. Ya lura cewa gwamnatin jihar, tare da haɗin gwiwa da gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro, tana aiwatar da ƙarin matakai don kare al’ummomin da ke cikin mawuyacin hali daga hare-hare.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar
Next Post: Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ?

Karin Labarai Masu Alaka

Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.