Dawo da jakadun Amurka da yawa gida da shugaba Donald Trump ya yi, zai kawo gibi ga manya masu wakiltar kasar a fiye da rabin kasashen saharar Afirka, abin da zai dagula kokarin da Amurkan ke yi na wanzar da wani tsari a yankin da Yayi fama da juyin mulki, da yake-yake a baya bayannan.
Tun bayan hawar sa kujerar mulki, gwamnatin Trump ta mai da hankalin ta ne kan aiwatar da diplomassiyar kasuwanci a Afirka, inda ta sauya daga bada tallafi zuwa cinikayya.
Trump ya nemi wanzar da zaman lafiya, da yarjejeniyar kasuwanci, da kuma samun amincewar bangarorin biyu, maimakon kai taimako kai tsaye.
Trump na bugun gaba cewa Amurka ita ce mafi dacewa wajen kawance da kasashen Afirka fiye da China, inda yaje yana da kudurin karfafa kawance, a wani yunkuri na kawar da tunanin da ake na ganin cewa Amurka ta yi watsi da Nahiyar inda China take kara shiga harkokin tattalin arziki.


