Hukumar Hisbah a jihar Katsina dake Najeriya ta gudanar da aikin ƙona giyar da aka kama a garin Bakori da ke shiyyar Funtua
Sanarwar ta ce Kwamandan Hisbah na Karamar Hukumar Dandume, DC Bashir Lawal Balarabe, tare da sauran kwamandojin Hisbah na shiyyar Funtua, sun halarci taron inda suka jagoranci lalata giyar da aka kama.
Sanarwar ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne domin dakile ayyukan da suka saɓa wa koyarwar addinin Musulunci da kuma kare tarbiyyar al’umma.
Taron ya samu halartar shugabannin Hisbah da malamai da dama, inda aka gabatar da wa’azi kan illar shan giya a addinin Musulunci.


