Kasar Iran na neman kulla yarjejeniya kan makaman nukiliya da Amurka, wadda zata samar da amfani ga tattalin arzikin duka kasashen biyu, a cewar wani jami’in jakadancin Iran a ranar Lahadi. Wannan ya biyo kwanaki kafin zaman tattaunawa ta biyu tsakanin Washington da Tehran.
A farkon wannan watan ne Iran da Amurka suka sabunta sake zama don tattaunawa kan shawo kan takaddamar da suka dade suna yi game da Shirin makaman nukiliya na Iran, don kuma su kaucewa barkewar yaki tsakanin kasashen biyu.
Amurka dai ta aike da jirgin ruwa mai dakon jiragen yaki zuwa yankin gabas ta tsakiya a karo na biyo, kuma tana shirin daukan matakin soji na zuwa lokaci mai tsawo idan tattaunawar bata yi nasara ba.
Sakataren harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio ya ce shugaba Donald Trump Yafi son a bi matakan diplomasiyya da tattaunawa kan kawo sulhu, amma ya nunan karara hakan ba lalle ya yiwu ba.


