Jakadan Amurka a Poland, ya yanke hulda da kakakin majalisar kasar a ranar Alhamis, yana zargin kakakin majalisar cewa ya zagi shugaban Amurka Donald Trump, bayanda ya soki manufofin gwamnatin shugaban na Amurka, da kuma kin goyon bayan a baiwa Trump Lambar yabo ta Nobel.
Wakilan gwamnatin hadin guiwa a Poland suna tsaka mai wuya a kokarin su na lallaba dangantakar su da shugaba Trump a gefe daya kuma su masu ra’ayin turai ne.
Musayar zazzafar kalamai a shafukan dandalin sada zumunci na X, ya jawo PM kasar Poland Donald Tusk, wanda yace “Ambasada Rose, kawaye suna mutunta juna ne, ba yi wa juna laccha ba, Akalla dai mu a Poland haka muka fahimci abunda kawance yake nufi.”
Kakakin majalisar dokokin Poland, ya fada ranar Litinin cewa, ba zai goyi bayan kudurin da kakakin majaisar dokokin Amurka Mike Johnson, dana Isra’ila suka gabatar na neman hada kan shugabannin majalisun kasashe su goyi bayan yakin neman a baiwa shugaba Donald Trump lambar yabo ta Nobel.

