Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin
Published: December 9, 2025 at 3:25 AM | By: Ibrahim Alfah Ahmad

Hukumomin Jamhuriyar Benin, sun fada jiya litinin cewa hare-haren da jiragen saman yaki na Najeriya suka kai sune suka gurgunta yunkurin juyin mulki a kasar, inda sojoji masu bore suka yi kokarin kama shugaba Patrice Talon.

Sojoji masu yunkurin juyin mulkin sun samu isa dab da Shugaba Talon, wanda ya gane ma idanunsa ba-ta-kashi tsakaninsu da masu gadinsa, kuma har sun iya suka kama wasu manyan hafsoshin soja guda biyu wadanda ba a sako su ba sai jiya litinin da safe.

Wadannan bayanan suna kumshe a cikin wata sanarwar da gwamnatin Jamhiriyar Benin ta wallafa game da yunkurin juyin mulkin, a bayan wani zaman majalisar ministocinta.

Sanarwar ta ce jiragen saman yakin Najeriya sun kai hare-hare suka lalata motocin yaki masu sulke na sojoji masu juyin mulkin, ba tare da sun kashe wani ba. Daga bisani, wasu zaratan sojoji daga kasar Cote D’Ivoire sun isa Cotonou, inda aka girka su domin daukar mataki ko da boren sojojin zai ci gaba.

Sojojin da suka yi yunkurin juyin mulkin sun fito daga sansanin soja na Togbin, inda tun kafin ketowar alfijir na ranar lahadi suka fara yada zango a gidan babban hafsan sojojin kasar, Janar Bertin Bada. An kashe matar janar din a gwabzawar da aka yi a wurin, amma hafsan ya samu ya tsere musu.

Sojojin sun samu suka kama babban hafsan sojojin kasa, Janar Abou Issa da Kanar Faizou Gomina, wadanda gwamnatin Benin ta ce an sako su daga bisani jiya litinin da safe a garin Tchaourou na arewacin kasar.

Masu yunkurin juyin mulkin, sun je suka kwace gidan telebijin na wani dan lokaci kafin a kore su, inda suka koma barikin Togbin, inda sojoji masu biyayya ga gwamnati da kuma jiragen saman yakin Najeriya suka yi ta far musu.

Har yanzu babu labarin inda Kanar Tigri Pascal yake, watau mutumin da aka ce shine jagoran masu yunkurin juyin mulkin.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio
Next Post: Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne

Karin Labarai Masu Alaka

An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
  • Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.