Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin
Published: December 9, 2025 at 3:25 AM | By: Ibrahim Alfah Ahmad

Hukumomin Jamhuriyar Benin, sun fada jiya litinin cewa hare-haren da jiragen saman yaki na Najeriya suka kai sune suka gurgunta yunkurin juyin mulki a kasar, inda sojoji masu bore suka yi kokarin kama shugaba Patrice Talon.

Sojoji masu yunkurin juyin mulkin sun samu isa dab da Shugaba Talon, wanda ya gane ma idanunsa ba-ta-kashi tsakaninsu da masu gadinsa, kuma har sun iya suka kama wasu manyan hafsoshin soja guda biyu wadanda ba a sako su ba sai jiya litinin da safe.

Wadannan bayanan suna kumshe a cikin wata sanarwar da gwamnatin Jamhiriyar Benin ta wallafa game da yunkurin juyin mulkin, a bayan wani zaman majalisar ministocinta.

Sanarwar ta ce jiragen saman yakin Najeriya sun kai hare-hare suka lalata motocin yaki masu sulke na sojoji masu juyin mulkin, ba tare da sun kashe wani ba. Daga bisani, wasu zaratan sojoji daga kasar Cote D’Ivoire sun isa Cotonou, inda aka girka su domin daukar mataki ko da boren sojojin zai ci gaba.

Sojojin da suka yi yunkurin juyin mulkin sun fito daga sansanin soja na Togbin, inda tun kafin ketowar alfijir na ranar lahadi suka fara yada zango a gidan babban hafsan sojojin kasar, Janar Bertin Bada. An kashe matar janar din a gwabzawar da aka yi a wurin, amma hafsan ya samu ya tsere musu.

Sojojin sun samu suka kama babban hafsan sojojin kasa, Janar Abou Issa da Kanar Faizou Gomina, wadanda gwamnatin Benin ta ce an sako su daga bisani jiya litinin da safe a garin Tchaourou na arewacin kasar.

Masu yunkurin juyin mulkin, sun je suka kwace gidan telebijin na wani dan lokaci kafin a kore su, inda suka koma barikin Togbin, inda sojoji masu biyayya ga gwamnati da kuma jiragen saman yakin Najeriya suka yi ta far musu.

Har yanzu babu labarin inda Kanar Tigri Pascal yake, watau mutumin da aka ce shine jagoran masu yunkurin juyin mulkin.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio
Next Post: Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.