Kasar Isra’ila ta share wani fili a kudancin gaza don gina sansani da zata aje falasdinawa, da watakila za’a sawa na’urorin leken asiri, da kuma na’uraro masu fasahar gane fuskokin mutane, a wajen shiga a cewar wani janar na sojan Isra’ila me ritaya.
Sojan sa kai, brigadier janar Amir Avivi me ritaya, ya shaidawa kamfanin Dillacin labarai na Reuters cewa za’a gina sansanin a Rafah inda aka babbaje ramukan da mayakan Hamas suka gina, kuma ma’aikatan Isra’ila zasu rika lura da shige da ficen wurin.
Avivi, shine wanda ya kafa kungiyar dandalin tsaro da kariya na Isra’ila, da ke wakiltar dubbannan sojojin sa kai. Baya magana da yawun sojan Isra’ila, wandanda suka ki yin tsokaci game da abun. Ofishin prime ministan Isra’ila bai ce wani abu kan Shirin gina sanasani a Rafah ba.
Avivi ya ce za’a yi amfani da sansanin wajen bawa Falasdinawa dake da niyyar barin Gaza zuwa kasar Misra, ko kuma wadanda ke son zama a nan matsuguni.


