Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna
Published: February 14, 2026 at 7:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar Laraban da ta gabata ne kasar Malawi ta fara yiwa yara allurar rigakafin shan Inna, inda ma’aikatan lafiya ke bi ajujuwan makaranta suna diga wa yara maganin rigakafin a bakin su, da zata kare su daga cutar shan Inna.

Wannan na nuna cewa har yanzu ba’a kawar da cutar a duniya ba, wadda yawanci take kama yara, kuma tana iya jayo shanyewar jiki, duk da kokarin da Hukumar Lafiya ta Duniya tare da ‘yan hadin guiwa suka shafe shekaru 35 suna yi.

Jami’an kiwon lafiya sun amince cewa sau da dama sun yi kokarin zuwa gab da kawar da cutar, ciki har da a shekaru 5 da suka wuce, inda masu dauke da cutar 5 kacal aka samu a duniya.

Amma hukumar lafiya ta Duniya ta ce an Samu masu dauke da cutar 38 tsakanin watan Janairu zuwa watan Octobar shekara ta 2025, dukkan su kuma a kasashen Pakistan da Afghanistan, da kuma wasu 151 da allurar rigakafin shan inna ta haddasa musu cutar a kasashe 13.

Kiwon Lafiya, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya
Next Post: An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi

Karin Labarai Masu Alaka

Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa
  • Rundunar Sojin Amurka Zasu Kaiwa Iran Hari
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi
  • Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna
  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.