A ranar Litinin kasashen Saudi Arabia, Jordan da kasashen Haddadiyar Daular Larabawa sun yi Allah wadai da yunkurin da Isra’ila take yi na saukakawa ‘yan kasar ta yadda zasu samu matsuguni a yankunan yammacin kogin Jordan da ke mallakin Palastine.
Shawarar da majalisar tsaron Isra’ila ta yanke ranar Lahadi, zai saukakawa yahudawa wajen siyen filaye a yankin, kuma zai bawa Isra’ila karin karfin iko a guraren da a bisa zato suna karkashin ikon Palasdinawa ne, a cewar wasu manyan ministocin Isra’ila 2.
Daya daga cikin ministocin dake da ra’ayin tsananin kishin kasa, ministan kudi Bezalel Smotrich, da yake sanar da hukuncin, ya ce gwamnatin sa zata ci gaba da rushe ra’ayin wanzuwar kasar Palestine.
Wani jawabi daga ministocin kasashen gabas ta tsakiya da sauran kasahen larabawa, da suka hada da Masar da Turkiya sun yi Allah wadai da wannan kuduri, da ya karya dokokin kasa da kasa, kuma zai kawo kalubale ga mafitar da ake so a samu na kowanne bangare ya mallaki kasar sa, da kuma wanzuwar zaman lafiya a yankin.


