Hukumar kula da hakkin Bil’adama ta MDD tayi Allah wadai da kasar Iran ko Farisa a ranar jumma’a, kan keta hakkin Bil’adama, kuma ta bukaci da a gudanar da bincike kan murkushe masu zanga-zanga, mataki da ya halaka dubban mutane.
Shugaban hukumar, Volker Turk, wanda ya gayawa wakilan hukumar abubuwa da suka faru a Iran, a taron ta da aka yi a birnin Geneva, ya bayyana damuwarsa kan makomar wadanda hukumomin Iran suka kama lokacin zanga zangar.
Hukumar ta amince da wani kuduri da zai fadada kudurin da ta amince dashi tun a shekara 2022 na gudanar da bincike ciki har da na yanzu, da zummmar daukar mataki nan gaba.
Iran tayi Allah wadai da wannan mataki, tana mai cewa an tsoma siyasa cikin lamarin, tana ta nanata matakan gudanar da bicike, tace wannan mataki shishshige ne cikin harkokin cikin gida. Ta kuma aza laifin tarzomar “kan ‘yan ta’adda, da masu neman tada zaune tsaye, wadanda take zargi, kan ‘yan adawar gwamnattin kasar daga ketare da kuma kasashen Amurka da Isra’ila.
Kasashe 25 ne suka amince da wannan kuduri cikin su har da Faransa, da Mexico, da koriya ta kudu, yayinda kasashe bakwai ciki harda China, da India suka ki goyon bayan kudurin, wasu kasashe 14 kuma suka kauracewa jefa kuri’a.
Kasashen China, da Pakistan, da Ethiopia, duk sun bayyana rashin gamsuwa da tasirin zaman hukumar, har jakadan China a hukumar ya kira batun, “alamarin cikin gida ne na Iran.


