Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran
Published: January 26, 2026 at 7:39 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da hakkin Bil’adama ta MDD tayi Allah wadai da kasar Iran ko Farisa a ranar jumma’a, kan keta hakkin Bil’adama, kuma ta bukaci da a gudanar da bincike kan murkushe masu zanga-zanga, mataki da ya halaka dubban mutane.

Shugaban hukumar, Volker Turk, wanda ya gayawa wakilan hukumar abubuwa da suka faru a Iran, a taron ta da aka yi a birnin Geneva, ya bayyana damuwarsa kan makomar wadanda hukumomin Iran suka kama lokacin zanga zangar.

Hukumar ta amince da wani kuduri da zai fadada kudurin da ta amince dashi tun a shekara 2022 na gudanar da bincike ciki har da na yanzu, da zummmar daukar mataki nan gaba.

Iran tayi Allah wadai da wannan mataki, tana mai cewa an tsoma siyasa cikin lamarin, tana ta nanata matakan gudanar da bicike, tace wannan mataki shishshige ne cikin harkokin cikin gida. Ta kuma aza laifin tarzomar “kan ‘yan ta’adda, da masu neman tada zaune tsaye, wadanda take zargi, kan ‘yan adawar gwamnattin kasar daga ketare da kuma kasashen Amurka da Isra’ila.

Kasashe 25 ne suka amince da wannan kuduri cikin su har da Faransa, da Mexico, da koriya ta kudu, yayinda kasashe bakwai ciki harda China, da India suka ki goyon bayan kudurin, wasu kasashe 14 kuma suka kauracewa jefa kuri’a.

Kasashen China, da Pakistan, da Ethiopia, duk sun bayyana rashin gamsuwa da tasirin zaman hukumar, har jakadan China a hukumar ya kira batun, “alamarin cikin gida ne na Iran.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya
Next Post: Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
Kasar Ghana Ta Bayyana Fataucin Bayi A Matsayin Babban Laifi Afrika
Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.