Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP
Published: January 24, 2026 at 5:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada tsayuwar sa kan akidun sa na siyasa, yana mai cewa ba zai sayar da ƙa’idojinsa domin amfanin kansa ba.

Kwankwaso ya bayana hakan ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da wasu shugabannin ƙananan hukumomi, wasu ’yan Majalisar Wakilai da wasu mataimaka, sun fice daga jam’iyyar NNPP.

Da yake jawabi ga magoya baya a gidan sa da ke Kano jim kaɗan bayan murabus ɗin gwamnan a ranar Juma’a, Kwankwaso ya ce gwagwarmayar sa ta siyasa tun farko ta ta’allaka ne kan ’yantar da talakawan Najeriya.

“Ni ba na sayarwa ba ne. Akidun siyasar mu ne ke tsayar da ni a kan hanya. Da ace neman riba ta kaina nake yi, da tuni na bi hanya mai sauƙi, kuma da ba ku same ni a nan ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar Kwankwasiyya ta tsaya tsayin daka ne bisa ɗabi’u da manufofi na bai ɗaya, ba wai saboda abin duniya ba.

“Manufa da hangen nesan mu ne ke ƙarfafa ni. Da ace kwaɗayi ne ke motsa ni, da tuni na karɓi kuɗi na gudu, kuma da ba ku zo nan nuna goyon baya ba,” ya ƙara da cewa.

Kwankwaso ya kuma buƙaci magoya bayan sa da su fara shiri da wuri gabanin zaɓukan gama-gari na 2027, yana mai gargaɗi kada a yi sakaci.

“Muna buƙatar mutane irin ku da suka sadaukar kuma suka tsaya kan gaskiya. Kada ku yi kasa a gwiwa, domin wata rana za mu cimma burinmu,” in ji shi.

Da yake magana kan abubuwan da ke faruwa a Kano a baya-bayan nan, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya jaddada muhimmancin fara shirye-shirye tun yanzu.

“Duba da abin da ke faruwa a Kano a yau, dole ne mu fara shiri, domin akwai mutanen da suka kuduri aniyar rusa abin da muka gina tsawon lokaci,” in ji shi.

“Manufa ta ita ce yaƙi don kare talakawa a kowane lokaci. Ba zan yi sulhu da masu cin zarafin jama’a ba,” in ji shi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida
Next Post: Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.