Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP
Published: January 24, 2026 at 5:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP kuma jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sake jaddada tsayuwar sa kan akidun sa na siyasa, yana mai cewa ba zai sayar da ƙa’idojinsa domin amfanin kansa ba.

Kwankwaso ya bayana hakan ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da wasu shugabannin ƙananan hukumomi, wasu ’yan Majalisar Wakilai da wasu mataimaka, sun fice daga jam’iyyar NNPP.

Da yake jawabi ga magoya baya a gidan sa da ke Kano jim kaɗan bayan murabus ɗin gwamnan a ranar Juma’a, Kwankwaso ya ce gwagwarmayar sa ta siyasa tun farko ta ta’allaka ne kan ’yantar da talakawan Najeriya.

“Ni ba na sayarwa ba ne. Akidun siyasar mu ne ke tsayar da ni a kan hanya. Da ace neman riba ta kaina nake yi, da tuni na bi hanya mai sauƙi, kuma da ba ku same ni a nan ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar Kwankwasiyya ta tsaya tsayin daka ne bisa ɗabi’u da manufofi na bai ɗaya, ba wai saboda abin duniya ba.

“Manufa da hangen nesan mu ne ke ƙarfafa ni. Da ace kwaɗayi ne ke motsa ni, da tuni na karɓi kuɗi na gudu, kuma da ba ku zo nan nuna goyon baya ba,” ya ƙara da cewa.

Kwankwaso ya kuma buƙaci magoya bayan sa da su fara shiri da wuri gabanin zaɓukan gama-gari na 2027, yana mai gargaɗi kada a yi sakaci.

“Muna buƙatar mutane irin ku da suka sadaukar kuma suka tsaya kan gaskiya. Kada ku yi kasa a gwiwa, domin wata rana za mu cimma burinmu,” in ji shi.

Da yake magana kan abubuwan da ke faruwa a Kano a baya-bayan nan, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar ya jaddada muhimmancin fara shirye-shirye tun yanzu.

“Duba da abin da ke faruwa a Kano a yau, dole ne mu fara shiri, domin akwai mutanen da suka kuduri aniyar rusa abin da muka gina tsawon lokaci,” in ji shi.

“Manufa ta ita ce yaƙi don kare talakawa a kowane lokaci. Ba zan yi sulhu da masu cin zarafin jama’a ba,” in ji shi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida
Next Post: Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur Afrika
  • Majalisa A Kasar Somaliya Ta Amince Da Sauya Tsarin Mulkin Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.