A Najeriya an kashe akalla mutane 34 a ranar talata a wasu jerin hare hare da ‘yan binidga masu ikirarin Islama da ake kira Lakurawa suka kai wasu kauyuka a jihar kebbi dake arewa maso yammacin kasar, kamar yadda rahotannin tsaro da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani.
Lakurawa wata sabuwar Kungiyar mayakan sakai ce wacce galibi take aika-aika a jihohin kebbi da sakkwato, yankin da Amurka ta auna hare hare kan kunigyoyi da suke da alaka da ISIS cikin watan Disambar bara.
Wannan harin na ‘yan bindigar yana da alamun ayyukan Kungiyar, inda mahara za su farwa kananan kauyuka masu yawa a lokaci daya saboda su dagula hankalin masu aikin tsaro, su Tilastawa kauyawa su gudu.
Rahotannin suka ce an kashe mutane 16 a wuri da ake kira Mamunu mutum biyar a Awashaka, 3 a Masama, sannan mutane biyu-biyu a wasu kauyuka biyar.
Rahoton yace jami’an tsaro sun dira a yankin domin kare mutane, su taimaki wadanda suka tsira, da kuma toshe hanyoyin da mayakan sakan suke bi domin su gudu.


