Magajin garin Istanbul na kasar Turkiyya, dake garkame a gidan kurkuku kusan shekara daya Ekrem Imamoglu ya yi kira ga shugaba Tayyib Erdogan da ya gudanar da zabe yanzu, kuma yayi hasashen cewa shugaban zai fadi idan ya kara tsayawa takara, a lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Reuters.
A shekarun baya-bayannan Imamoglu ya fito a matasayin babban dan adawar Erdoyan, inda kididdigar ra’ayin masu zabe, ke nuna cewa idan zai iya tsayawa takara lalle zai iya ka da shugaban na Turkiya da ya shafe fiye da shekaru 20 kan mulki.
Amma gwamnatin kasar ta mai da hankali a kan sa wajen daukan mataki maitsanani da take yi kan abokan hamayyar siyasa.
Imamoglu ya tsinci kan sa a gidan kaso tun a watan Maris din bara yana jiran a gurfanar da shi gaban kotu, inda ake tuhumar sa da almundahana, abin da ya musanta.


