Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai
Published: December 16, 2025 at 7:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 16, 2025

Majalisar wakilan tarayyar Najeriya ta jefa kuri’ar amincewa da sanya baki wajen binciken rikicin da ya barke a tsakanin hukumar kula da jigila da tace danyen man fetur ta Najeriya da matatar mai ta Dangote, a sanadiyyar munakisar bayar da lasisin shiga da tataccen mai cikin kasar, da kuma kayyade farashinsa, yayin da ake zargin shugaban hukumar da wawurar makudan kudade.

Attajirin da ya fi kowa arzikin kudi a Najeriya, Aliko Dangote, ya zargi wannan hukuma da laifin bada lasisin shiga kasar da tataccen man fetur maras kyau da nufin gurgunta matatun tace man fetur na kasar, ciki har da mai tace ganga dubu 650 ta mai a kullum dake Lagos, wadda ita ce kuma mafi girma a duk fadin nahiyar Afirka.

Dangote ya bukaci da a gudanar da bincike akan shugaban hukumar Farouk Ahmed, wanda yayi zargi da rashin iya tafiyar da aiki, da kuma yadda ya kashe dubban miliyoyin Naira wajen tura ‘ya’yansa hudu karatun sakandare a kasar Switzerland, kudin da ba ya da wata hanyar da aka sani ta halal ta samu.

‘Yan majalisa sun yi kashedin cewa wannan rikici a tsakanin Dangote da hukumar yana iya haddasa karancin mai a daidai lokacin da ake tinkarar bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara, kuma tababa a kan hukumar kula da jigila da tace man na barazana ga tabbatar da samuwar makamashi da kashe kwarin guiwar masu zuba jari a fannin.

‘Yan majalisar suka ce matatar mai ta Dangote mai matukar muhimmanci ce ga tabbatar da tsaron makamashi a kasa wadda zata kawo karshen dogaron da Najeriya take yi a kan shigo da tataccen mai, da samarwa da kasar kudaden wajen da take matukar bukata, da ma sauko da farashin mai a cikin gida.

Ba a bayyana ranar da Kwamitin kula da harkokin man fetur na majalisar zai yi zama kan wannan batun ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA
Next Post: ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi

Karin Labarai Masu Alaka

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.