Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi
Published: December 5, 2025 at 7:57 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 5, 2025

Najeriya ta amince da biyan kudi Naira biliyan 185 ga kamfanonin samar albarkatun mai da suke bin ta bashi da irin gas da suke samarwa ga injunan samar da wutar lantarki a kasar, domin karfafa bangaren makamashi da inganta samar da wutar lantarki.

Majalisar Tattalin Arziki ta Kasa dake karkashin jagorancin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima, ita ce ta amince da biyan kudin bayan shugaba Bola Tinubu ya bayarda umurnin a biya wadannan basussukan dake neman gurgunta mai da gas da ake bukata ga masana’antun samar da wutar lantarki a kasar.

Karamin ministan man fetur Ekperikpe Ekpo, ya ce za a biya wadannan basussuka ne ta hanyar Zarmiya, wato kamfanonin zasu cire wadannan kudade daga kudaden da ya kamata su biya gwamnati na man da suke dauka daga kasar

Najeriya, kasar da ta fi kowacce yawan jama’a a nahiyar Afirka, tana ci gaba da fuskantar karancin wutar lantarki da aka kasa shawo kansa shekara da shekaru, abinda ke dakushe harkokin kasuwanci da na tattalin arzikin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya
Next Post: Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin Labarai
Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
  • Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Chelsea Tayi Kaca-Kaca Da Barcelona A Gasar UCL Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.