Ministan tsaro ya umarci janye sojoji daga shingayen bincike a Titunan kasar.
Ministan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayar da umarnin gaggawa na janye dakarun sojoji daga wuraren binciken ababan hawa da ke manyan tituna a sassa daban-daban na ƙasar.
Ya bayyana cewa wannan matakin na da nufin mayar da hankali kan yaƙi da ’yan ta’adda da sauran barazanar tsaro a sassa daban-daban na ƙasar, inda jami’an ’yan sanda za su karɓi ragamar kula da shingayen tituna da tsaron ababan hawa.
Ministan ya ce sojoji za su koma ayyukan su na ƙwarai na yaƙi da ta’addanci da samar da tsaro a yankunan da ke fama da barazana, musamman Arewa maso Gabas da wasu sassan Arewa ta Tsakiya.
Ya kuma jaddada cewa hakan ba yana nufin raguwar tsaro ba ne, domin an tsara yadda za a maye gurbin sojojin da jami’an ƴan sanda da suka samu horo musamman kan kula da jama’a da tabbatar da doka a tituna.


