Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna
Published: December 12, 2025 at 11:20 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 12, 2025

Ministan tsaro ya umarci janye sojoji daga shingayen bincike a Titunan kasar.

Ministan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya bayar da umarnin gaggawa na janye dakarun sojoji daga wuraren binciken ababan hawa da ke manyan tituna a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya bayyana cewa wannan matakin na da nufin mayar da hankali kan yaƙi da ’yan ta’adda da sauran barazanar tsaro a sassa daban-daban na ƙasar, inda jami’an ’yan sanda za su karɓi ragamar kula da shingayen tituna da tsaron ababan hawa.

Ministan ya ce sojoji za su koma ayyukan su na ƙwarai na yaƙi da ta’addanci da samar da tsaro a yankunan da ke fama da barazana, musamman Arewa maso Gabas da wasu sassan Arewa ta Tsakiya.

Ya kuma jaddada cewa hakan ba yana nufin raguwar tsaro ba ne, domin an tsara yadda za a maye gurbin sojojin da jami’an ƴan sanda da suka samu horo musamman kan kula da jama’a da tabbatar da doka a tituna.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
Next Post: Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026

Karin Labarai Masu Alaka

Ga Fili Ga Doki Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.