Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa
Published: December 1, 2025 at 5:12 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 1, 2025

Dr. Usman Isiyaku, mai sharhi akan al’ammuran yau da kullum, shugabanci na gari, ya ayyana wasu kadan daga cikin tsare-tsaren na gwamnatin Tinubu, a kan al’ammurra da suka shafi jagorancin Najeriya.

Inda yake cewa “Bisa ga al’adar gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, ba wani abun mamaki bane ko sabon abu, don ya nada Yarbawa, a mafi akasari da mukamai masu girma. Idan aka duba za’a ga cewar tun fara mulkin shi da irin wannan salon ya fara.”

A wasu lokutta kuwa akan ga cewar Arewa tana da girma, don haka idan aka bata wasu tsirarun mukamai sai aga kamar an yi mata wata hikima. Sau da yawa ‘yan Arewa dake tare da gwamnatin ta shi, basu da wani karfi da za su iya gaya mishi gaskiya. Mafi akasari ma ‘yan abi yarima ne a sha kida.

Don kuwa da yawa daga cikin su, ba wai tunanin kasar ne a zukatan su ba, mafi akasari son kansu da nasu ne a zukatansu. Bugu da kari, duk wani abu da za’a gani a wannan gwamnatin, to yana da alaka da gwamnatin da ta gabata, ta Margayi Muhammadu Buhari.

Tsari ne da ba’a la’akari da cancanta wajen zabo wadanda zasu wakilci kasa, ko jama’a. Don haka ba wani abun mamaki bane don anga nadin jakadu na bangaren Yarbawa da basu da kwatankwacin kashi 10 na adadin yawan mutan Arewa, amma suke da jakadu 11 kana aka kai su kasashe manya a duniya.

Inda ita kuma Arewa ta tashi da jakadu 5 daga bangaren Arewa maso yamma, sai 5 daga Arewa maso gabas, kana wasu 5 da ke wakiltar Arewa ta tsakiya. Abun ala’akari a nan shine, yawan mutane da suka fito daga Arewa maso yamma da ke da jihohi 7, sun fi yawan mutane da suka fito daga baki daya Kudu maso Yamma da aka basu jakadu 11.

Haka kuma, wannan gwamnati ce da take la’akari da mutane da suka wahalar mata koda kuwa basu cancanta, da kuma mutane da suka fito daga bangare daya, ko kuwa bangaranci na addini, da na kabilanci, wanda ta haka ne zai ba mutum damar samu wani babban matsayi, ba la’akari da irin gudunmawar da zaka bada ake yi ba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Next Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”

Karin Labarai Masu Alaka

Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ribadu: Najeriya Ce Kasa Daya Tilo Da Ke Tabbatar Da Demokraɗiyya A Sahel Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • Kirana Ga ‘Yan Siyasar Arewa, Su Jira Sai 2031- Akume Labarai
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.