Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa
Published: December 1, 2025 at 5:12 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 1, 2025

Dr. Usman Isiyaku, mai sharhi akan al’ammuran yau da kullum, shugabanci na gari, ya ayyana wasu kadan daga cikin tsare-tsaren na gwamnatin Tinubu, a kan al’ammurra da suka shafi jagorancin Najeriya.

Inda yake cewa “Bisa ga al’adar gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, ba wani abun mamaki bane ko sabon abu, don ya nada Yarbawa, a mafi akasari da mukamai masu girma. Idan aka duba za’a ga cewar tun fara mulkin shi da irin wannan salon ya fara.”

A wasu lokutta kuwa akan ga cewar Arewa tana da girma, don haka idan aka bata wasu tsirarun mukamai sai aga kamar an yi mata wata hikima. Sau da yawa ‘yan Arewa dake tare da gwamnatin ta shi, basu da wani karfi da za su iya gaya mishi gaskiya. Mafi akasari ma ‘yan abi yarima ne a sha kida.

Don kuwa da yawa daga cikin su, ba wai tunanin kasar ne a zukatan su ba, mafi akasari son kansu da nasu ne a zukatansu. Bugu da kari, duk wani abu da za’a gani a wannan gwamnatin, to yana da alaka da gwamnatin da ta gabata, ta Margayi Muhammadu Buhari.

Tsari ne da ba’a la’akari da cancanta wajen zabo wadanda zasu wakilci kasa, ko jama’a. Don haka ba wani abun mamaki bane don anga nadin jakadu na bangaren Yarbawa da basu da kwatankwacin kashi 10 na adadin yawan mutan Arewa, amma suke da jakadu 11 kana aka kai su kasashe manya a duniya.

Inda ita kuma Arewa ta tashi da jakadu 5 daga bangaren Arewa maso yamma, sai 5 daga Arewa maso gabas, kana wasu 5 da ke wakiltar Arewa ta tsakiya. Abun ala’akari a nan shine, yawan mutane da suka fito daga Arewa maso yamma da ke da jihohi 7, sun fi yawan mutane da suka fito daga baki daya Kudu maso Yamma da aka basu jakadu 11.

Haka kuma, wannan gwamnati ce da take la’akari da mutane da suka wahalar mata koda kuwa basu cancanta, da kuma mutane da suka fito daga bangare daya, ko kuwa bangaranci na addini, da na kabilanci, wanda ta haka ne zai ba mutum damar samu wani babban matsayi, ba la’akari da irin gudunmawar da zaka bada ake yi ba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Next Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.