Hukumomi a kasar Kenya sun ce ma’aikatan agaji sun yi ta tsamo gawarwaki daga ruwan ambaliya a sassan birnin Nairobi tun daga ran asabar, a bayan ruwa kamar da bakin kwarya da ya haddasa ambaliya ya kashe mutane akalla 23, ya tafi da motoci tare da gurgunta zirag-zirgar jiragen sama a filin jirgi mafi girma a yankin gabashin Afirka.
Shugaba William Ruto na Kenya ya ce ya tura ma’aikatan gaggawa cikinsu har da sojoji domin gudanar da ayyukan ceto, yayin da ya mika taaziyya ga iyalan wadanda abin ya shafa.


