Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Published: November 30, 2025 at 3:34 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Mataimakin Shugaban jami’ar jihar Gombe Ferfesa Sani Yauta ya kaddamar da littafi mai take Sauye-Sauye a bangaren ilimi da shugabanci.

Jami’ar Gombe (GSU) ta gudanar da bikin kaddamar da sabon littafi mai suna “Dynamics of Educational Administration and Planning” wanda Farfesa Sani Ahmed Yauta ya rubuta, a dakin taro na Haruna Kadir Rasheed dake jami’ar.

Taron ya sami halartar jami’an gwamnati, malamai, da baki na musamman.

Shugaban taron, mataimakin Gwamnan Jihar Gombe, Dr. Manassah Daniel Jatau, ya yabawa Farfesa Yauta bisa wannan gudummawar ilimi da ya bayar a sashin ilimi.

Fitattun jami’an gwamnati sun halarci bikin, ciki har da shugaban ma’aikata na jihar Gombe, Alhaji Ahmed Kasimu Abdullahi, Shugaban Jami’ar Tarayya dake Kashere, Farfesa Umaru Pate, Shugaban Jami’ar Lincoln University, Farfesa Adamu Sadiq Abubakar da Shugabar kwalejin koyon jinya, tare da wasu shugabannin cibiyoyi a jihar.

Haka zalika, Daraktan Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Farfesa Yusuf Muhammed Abdullahi, ya hallarci bikin tare da sauran manyan baki.

A jawabin sa, Babban Mai Kaddamarwa, Arc. Yunusa Yakubu, ya jinjina wa Farfesa Yauta kan jajircewarsa wajen bunkasa ilimi, yana mai bayyana littafin a matsayin abin dogaro ga masu gudanarwa, masu bincike da masu tsara manufofin ilimi.

Littafin dai wata dama ce da mahukunta zasu iya amfani da ita don sabutan tsari da manhajoji da ake amfani da su a makarantu a kasar baki daya. An kuma ja hankalin sauran malamai a fannin ilimi da su bada irin wadannan gudumawar don habaka ilimi, da ganin an samar da yanayi wanda ilimi a kasar zai yi gogayya da kasashe masu cigaba a fanin ilimi.

Kabatar da kasidu da taron karawa juna sani irin wadannan na da matukara muhimanci ga cigaban ilimi, ta haka ma ana iya sako daliban ilimi wajen shirya irin wadannan tarukan, da muna musu makamar aiki; a cewar daya daga cikin mahalarta taron.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Next Post: Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana Kimiya
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.