Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
Published: July 10, 2026 at 9:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da sakatariyar wucin gadi ta ƙungiyar a birnin Kaduna, tare da yin kira ga shugabannin Arewa da su ƙara haɗa kai domin magance matsalolin tsaro, tattalin arziki da ci gaban da yankin ke fuskanta.

An ƙaddamar da sakatariyar ne a gini mai lamba 26 da ke kan titin Muhammadu Buhari Way, tsohuwar WAFF Road, inda kuma aka miƙa motocin aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa kafa sakatariyar wani muhimmin mataki ne na ƙarfafa ayyukan ƙungiyar da samar da ingantaccen tsari na daidaita manufofi da shirye-shiryen ci gaban jihohin Arewa 19.

Ya ce lokaci ya yi da shugabannin Arewa za su gina kan kyawawan tubalan da magabatan yankin suka kafa, tare da nuna jajircewa da sadaukarwa wajen magance ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

Gwamnan ya jaddada cewa halin da Arewa ke ciki na buƙatar haɗin kai da ɗaukar matakai cikin gaggawa, yana mai bayyana cewa aiwatar da tsare-tsaren da ƙungiyar ta tsara zai taimaka wajen shawo kan matsalolin yankin.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris, ya sake tabbatar da aniyar gwamnonin Arewa na ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tunkarar matsalolin yankin. Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa jagorancinsa wanda ya haifar da kafa sakatariyar ƙungiyar.

Shi ma Babban Daraktan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Dakta Ezekiel Gomos, ya ce sabuwar sakatariyar za ta inganta gudanar da ayyuka, daidaita manufofi da shirye-shiryen ƙungiyar, tare da ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin ƙungiyar da sauran hukumomin yankin da na ƙasa.

Ya gode wa Gwamna Inuwa Yahaya da sauran gwamnonin Arewa bisa goyon bayan da suka bayar, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da sakatariyar da motocin aikin cikin gaskiya da inganci domin cimma manufofin ƙungiyar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
Next Post: APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
  • Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.