Majalisar Mai Alfarma sarkin Musulmi Muhammadu Saad Abubakar na III ta tabbatar da cewa ba a ga Watan Shawwal ba a dukkanin fadin Najeriya don haka za a cika azumi.

Bisa haka Majalisar ta ayyana ranar Jumu’a 20 ga Watan Maris a matsayin 1 ga Watan Shawwal kuma ranar sallah ƙarama.
Mai alfarma sarkin Musulmi kuma ya bukaci al’ummar musulmi da su ci gaba da yin ibadoji da ayyukan alkhairi a kowane lokaci tare da ci gaba da addu’o’i ga shugabanni don samun zaman lafiya da aminci da kwanciyar hankali.


