Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na
Published: January 5, 2026 at 7:41 AM | By: Bala Hassan

Sabon Shugaban ƙungiyar Kwallon Kafa ta Wikki Tourist FC Bauchi dake tarayyar Najeriya Salmanu Abubakar yayi alkawarin kawo ci gaba a ƙungiyar.

Salmanu Abubakar ya ce tun kafin ya zo wannan matsayi dama ya san matsalolinta, domin ya rike matsayin Sakataren ƙungiyar magoya bayan Wikki.

Babban matsalar Wikki shine shishigi wajan shiga aikin da ba naka ba “in ji shi, a lokacin zantawarsu da wakilin GTA Hausa.

Saboda haka babban abunda ya farayi shine zama da ma’aikatan hukumar don gyara wannan lamari ta hanyar ko wa ya tsaya akan aikin sa, abunda bature ya ke ciwa (Division of labour) yin haka shine mataki gyara na farko wadda hakan zai kawo cigaba sosai.

Kan batun ‘yan wasa kuwa Salmanu yace ya dauki matakin gyara tun da dama rashin sanya kwallon a raga ita ce matsala to tuni ya gayyaci sabbin ‘yan wasa shida da zai’yi anfani da su a tsakiyar kakan wanan bana kuma kwaliya zata biya kudin sabulu wajan faranta wa magoya baya rai.

Ya kuma bada tabbacin zasu ba wa maihoras da ƙungiyar Abdullahi Maikaba, cikekken dama wajan gudanar da aikin sa don samun nasara wa ƙungiyar.

Salmanu yace kamar yadda maigirma Gwamnan jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, ya basu amana don gyara da kuma kawo cigaba a wannan Ƙungiyar to bazasu ci amanan maigirma Gwamnan ba wajan aiki tukuru don samun nasara a wannan Ƙungiyar ta Wikki Tourist FC.

Da ya ke tsokaci ga me da ƙungiyar magoya bayan Wikki Tourist, Salmanu Abubakar ya ce wannan shine babban kalu balen sa amman akwai shiri da yakeyi don tabbacin adalci a duk bangarorin jihar Bauchi wajan sanya musu wakili a cikin wannan ƙungiya, bayan haka akwai wata horaswa ta musamman da za’a basu wajan yadda zasu gudanar da aikin yayin wasanni.

Daga karshe yayi alkawarin dawo da ƙungiyar cikin hayyacinta a teburin gasar Firimiyar lig na Najeriya ganin yadda kungiyar a yanzu ta ke wani matsayi da bai da ce ba.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya
Next Post: Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25 Shirye-Shirye
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • “Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.