Gidan talabijin na KCNA, na kasar Koriya Ta Arewa, ya ruwaito cewa, jam’iyya mai Mulki ta kasar Koriya ta Arewa ta sake zaben shugaban kasar Kim Jong Un a matsayin babban sakataren jam’iyyar a rana ta hudu na taron majalisar wakilan kasar a ranar Lahadi.
A cikin wani rahoto na jinjinawa, ta yabawa Kim da daukaka martabar kasar, da samar da yanayi na kasa da kasa da ya dace da gwagwarmayar juyin juya hali da kuma karfafa sojojin kasar “zuwa manyan sojoji masu karfi.”
A karkashin jagorancinsa, “Shirin ko ta kwana na yaki da sojojin kasar suka samu da inganta makaman nukiliya ya saya zama abun yabo,” in ji KCNA.
Taron ya kuma zabi mambobin kwamitin tsakiya na jam’iyyar tare da yin kwaskwarima ga dokokin jam’iyyar, in ji KCNA. Bai bayar da cikakkun bayanai na canje-canjen ba.


