Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri
Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Janar O.O Oluyede, da Babban Hafsan Rundunar Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, sun isa birnin Maiduguri na Jihar Borno domin shaida yanayin da ake ciki na matsalar tsaro da kuma jajantawa al’ummar jihar Borno.
Ziyarar tasu na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 24 da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na tura dukkan hafsoshin tsaro zuwa Maiduguri, sakamakon jerin hare-haren ƴan ta’adda, ciki har da fashewar bama-bamai guda uku a yammacin ranar Litinin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 20 tare da jikkata fiye da 100.
Shugabannin sojojin sun sauƙa a sansanin sojin sama da ke Maiduguri, inda kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta yankin Arewa maso Gabas (Operation Hadin Kai), da sauran manyan hafsoshin soji suka karɓe su.
Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na magance ƙaruwar hare-haren ƴan ta’adda a jihar Borno, musamman bayan hare-haren bama-bamai na baya-bayan nan da ake zargin mayakan Boko Haram/ISWAP ne suka kai.
Tun da farko dai, Shugaba Tinubu ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda ya bayyana su a matsayin “ayyukan mugunta na ƙungiyoyin ta’addanci masu muguwar aniya,” tare da alƙawarin ƙara ƙaimi wajen yaƙar dukkan ƙungiyoyin ƴan ta’adda.
A halin yanzu, rundunar soji na ci gaba da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tsaro mai inganci a yankunan da abin ya shafa, ta hanyar ƙara sa ido da kuma ƙarfafa matakan tsaro.


