Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tsohon Dankarar Gwamnan PDP A Gombe Ya koma ADC
Published: December 18, 2025 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Muhammad Jibrin Barde, ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) gabanin zaɓen 2027.

Dan Barde ya bayyana hakan a daren ranar Talata a gidansa, inda ya nuna katin zamowa mamba na ADC, yana mai cewa ya dawo ne domin sabunta rajistar sa da jama’rsa

Ya ce ya bar PDP tun farkon shekarar 2025, yana jaddada cewa burinsa shi ne ceto jihar Gombe daga abin da ya bayyana a matsayin mulkin masu harkar kasuwanci.

“Ina tabbatar muku da cewa, kamar yadda kuka sani, ana samun gagarumar tafiya a faɗin ƙasar nan, wadda muka ba wa suna ‘Salon Tafiya’.

“Muna aiki a kan wannan tafiya tare da shugabanninmu a faɗin ƙasar, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, tsofaffin gwamnoni da ministoci.

“Manufar wannan tafiya ita ce ceto ƙasar nan daga halin da take ciki na rashin tsaro, matsin tattalin arziki da ƙarancin ababen more rayuwa,” in ji shi.

Jibrin Dan Barde ya ƙara da cewa, “Yana da muhimmanci mu dawo gida domin sabunta rajistar membobimmu kuma mun kuduri aniyar ci gaba da wannan tafiya, kuma yanzu ne lokacin da ya dace mu sake sabunta membobimmu.”

Dangane da haɗin kai, ya ce hadakar ta himmatu matuƙa wajen ceto jihar, yana nuna damuwa kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙaruwar rashin tsaro.

“Kamar yadda kuke gani, akwai ƙarancin ababen more rayuwa da kuma rashin tsaro, sannan wannan shine iri rashin ɗaukar alhaki ne muke son yaƙi a jihar nan.

“Muna son samar da shugabanci mai ma’ana, mu bai wa kowa damar cin nasara, mu inganta ilimi ba ilimin da mutum ɗaya ko ƙungiya ke sarrafawa kamar kamfani mai iyaka ba,” in ji shi.

Da yake bayyana dalilin komawa ADC, Dan Barde ya ce jam’iyyar na wakiltar sabon zamani, tare da kira ga wasu da su shigo cikinta.

“Abin da muke son yi yanzu shi ne sabunta membobimmu a ƙarƙashin sabon zamani, kuma ga waɗanda ba mambobi ba, muna kiran su da su shigo ADC domin mu tunkari wannan gwamnati mai ɗaukar alhaki,” in ji shi.

Haka kuma ya gargaɗi al’umma da kada su sayar da ƙuri’un su.

“Kada ku karɓi taliya ko Naira 500 ku sayar da ƙuri’unku yace waɗannan darussa ne masu muhimmanci da ya kamata mu koya

Siyasa

Post navigation

Previous Post: FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
Next Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
PDP Zata Karbi Mulki 2027 Inji Shugabannin Jam’iyar Siyasa
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba
  • Tsohon Dankarar Gwamnan PDP A Gombe Ya koma ADC
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka
  • Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
  • Zamu Hada Kai Mu Yaki Cutar Shan’inna (Polio) Labarai
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Jirgin Ya Fado Ne Da Maraice Kuma Ya Taso Daga Kaduna Zuwa Fatakol Sai Aka Sauya Masa Hanyar Zuwa Owerri Najeriya
  • Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.