Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC
Published: December 18, 2025 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 18, 2025

Ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Muhammad Jibrin Barde, ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) gabanin zaɓen 2027.

Dan Barde ya bayyana hakan a daren ranar Talata a gidansa, inda ya nuna katin zamowa mamba na ADC, yana mai cewa ya dawo ne domin sabunta rajistar sa da jama’rsa

Ya ce ya bar PDP tun farkon shekarar 2025, yana jaddada cewa burinsa shi ne ceto jihar Gombe daga abin da ya bayyana a matsayin mulkin masu harkar kasuwanci.

“Ina tabbatar muku da cewa, kamar yadda kuka sani, ana samun gagarumar tafiya a faɗin ƙasar nan, wadda muka ba wa suna ‘Salon Tafiya’.

“Muna aiki a kan wannan tafiya tare da shugabanninmu a faɗin ƙasar, ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar, tsofaffin gwamnoni da ministoci.

“Manufar wannan tafiya ita ce ceto ƙasar nan daga halin da take ciki na rashin tsaro, matsin tattalin arziki da ƙarancin ababen more rayuwa,” in ji shi.

Jibrin Dan Barde ya ƙara da cewa, “Yana da muhimmanci mu dawo gida domin sabunta rajistar membobimmu kuma mun kuduri aniyar ci gaba da wannan tafiya, kuma yanzu ne lokacin da ya dace mu sake sabunta membobimmu.”

Dangane da haɗin kai, ya ce hadakar ta himmatu matuƙa wajen ceto jihar, yana nuna damuwa kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙaruwar rashin tsaro.

“Kamar yadda kuke gani, akwai ƙarancin ababen more rayuwa da kuma rashin tsaro, sannan wannan shine iri rashin ɗaukar alhaki ne muke son yaƙi a jihar nan.

“Muna son samar da shugabanci mai ma’ana, mu bai wa kowa damar cin nasara, mu inganta ilimi ba ilimin da mutum ɗaya ko ƙungiya ke sarrafawa kamar kamfani mai iyaka ba,” in ji shi.

Da yake bayyana dalilin komawa ADC, Dan Barde ya ce jam’iyyar na wakiltar sabon zamani, tare da kira ga wasu da su shigo cikinta.

“Abin da muke son yi yanzu shi ne sabunta membobimmu a ƙarƙashin sabon zamani, kuma ga waɗanda ba mambobi ba, muna kiran su da su shigo ADC domin mu tunkari wannan gwamnati mai ɗaukar alhaki,” in ji shi.

Haka kuma ya gargaɗi al’umma da kada su sayar da ƙuri’un su.

“Kada ku karɓi taliya ko Naira 500 ku sayar da ƙuri’unku yace waɗannan darussa ne masu muhimmanci da ya kamata mu koya

Siyasa

Post navigation

Previous Post: FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca
Next Post: Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba

Karin Labarai Masu Alaka

Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
  • Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.