Yaki ta sararin samaniya da Amurka da Isra’ila suke yi kan Iran sun fadada shi ranar Litinin ba tare da sanin yau she zai so karshe ba, inda Isra’ila ta kai hari a Lebanon, a zaman martani ga harin da Hezbollah ta kai mata, sannan Iran tana ci gaba da kai hare hare da makamai masu linzami, da jiragen drones kan kasashe da suke yankin Gulf inda Amurka take da sansanonin.
Shugaban Amurka Donald Trump yace sai ta yiwu za’a ci gaba da yakin na tsawon makonni, tare da cewa ba’a san wanene mai fada a ji a Tehran ba, bayanda kisan shugaban addinin kasar Ayatollahi Ali Khameni, a farkon Farmakin na hadin guiwa da Amurka da Isra’ila suka kaddamar kan kasar.
Harin da Amurkan da Isra’ila suka kai kan Iran ya jefa yankin Gulf cikin yaki, yayi sanadin mutuwar mutane a Iran, da Isra’ila da lebanon, lamarin ya jefa zirga zirga da balaguro ta sama cikin yamutsi, da kuma rufe mashigin ruwa na Hormuz, inda kashi daya cikin biyar na mai da ake amfani a duniya yake bi kusada gabar ruwan Iran, wadda yasa farashin mai ya tashi.
Sakamakon yakin cibiyar gudanar yake yaki ta Amurka da ake kira Central Command da turanci, tace bisa kuskure Kuwait ta harbo jiragen yakin Amurka uku, amma duka ma’aikatan jirgin su shida sun tsallake rijiya da baya.


