Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe
Published: December 6, 2025 at 8:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta bayyana cewa ta kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a ayyukan masu garkuwa da mutane da kuma satar shanu a fadin jihar.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar dauke da sahannun Jami’in hulda da jama’a na rundunar DSP Buhari Abdullah, an kama Abdullahi Ibrahim mai shekaru 40 a garin Tilde dake karamar hukumar Funakaye, a ranar 23 ga Nuwamba, 2025, bayan samun sahihan bayanai daga wani mai kishin kasa da suka zargeshi da boye masu laifi.

A yayin bincike, Abdullahi ya amsa laifin sa, inda ya bayyana cewa yana da hannu a satar shanu da kuma wasu hare haren masu garkuwa da mutane a fadin jihar Gombe.

Haka kuma ya fadi sunayen wasu abokan aikin sa da suka hada kai wajen gudanar da miyagun ayyukan a jihohin Gombe, Bauchi, Yobe da jihar Adamawa.

Rundunar ta ce a bisa wannan bayani ne jami’an ‘yan sanda da ke Operation Hattara tare da hadin gwiwar kungiyar masunta na jihar Gombe suka kai samame a wasu maboyar miyagun, inda aka yi musayar wuta da suka kai ga cafke karin mutum shida.

Wadanda aka kama sun hada da, Usman Mohammed, mai shekaru 30,Hussain Idris, mai shekaru 37, Adamu Tukur, mai shekaru 37 ,Yau Abdullahi, mai shekaru 25 da Ali Umar, mai shekaru 18 sai Hassan Usman, mai shekaru 40 da kuma Abdullahi Ibrahim, mai shekaru 40, daga Tilde,Karamar Hukumar Funakaye jihar Gombe

Sannan Rundunar ta tabbatar da ci gaba da gudanar da bincike tare da shirin gurfanar da su a gaban kotu.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026.
Next Post: Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA.

Karin Labarai Masu Alaka

Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
  • Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.