Ministan harkokin cikin gidan kasar Ghana ya bada labarin cewa ‘yan tawaye masu ikirarin Islama a Burkina Faso sun kashe ‘yan kasar Ghanan su bakwai masu cinikin tumatur, a lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari kan wani gari da ake kira Titao dake arewacin Burkina Faso a ranar Asabar data gabata.
Mutanen da harin ya rutsa da su, suna cikin wata tawagar mutum 18 da suka shiga makwabciyar kasar daga arewa, domin su sari tumatur, lokacin da mayakan suka aukawa garin, suka rarrabe maza da mata, daga bisani suka bude musu wuta, kamar yadda ministan ya gayawa wata tashar gidan rediyon kasar.
Minista Mohammed Mubarak Muntaka yace “suka goce da harbe harbe, suka kashe kusan dukkan maza da suke wurin, suka kona gawarwakin su da babbar motar da suke ciki,” har ba’za iya shaida su ba.
Minista Muntaka yace maza uku da mace daya sun tsallake rijiya da baya tare da samun raunuka. Saura mata bakwai dake cikin ayarin sun tsere ba tare da sun jikkata ba.
Daga bisani ya dauki hukumomi a Burkina Faso sa’o’i masu yawa suka sake kwato iko kan garin, kamar yadda ministan ya fada, ya kara da cewa, jami’an na Burkina Fason, sunyi alkawarin bada kariyan soja ga sauran tawagar da wadanda suka jikkata zuwa ofishin jakadancin Ghana dake birnin Ouagadougou, babban birnin kasar ta Burkina Faso.


