Prime ministan kasar Senegal, Ousmane Sonko ya nemi a dabbaka dokar da zata ninka zama gidan kurkuku daga shekara 5 zuwa 10 ga duk wadanda aka kama da yin auren jinsi, da sauran abubuwa da suka jibanci irin wannan halayya.
Da yake jawabi ga majalisar kasar a ranar Talata, Sonko ya ce, dokar zata shafi duk wata dangantaka da bata dace ba tsakanin jinsin mutane daya, kuma duk wanda aka kama yana irin wannan alaka da wanda bai kai shekaru 21 ba, zai fuskanci cikakken hukunci.
Wadanda aka kama da laifi kuma zasu iya fuskantar tara daga sefa miliyan biyu zuwa miliyan 10 wanda yayi daidai da dala 3,590 zuwa dala 17,953.
Sonko yayi kira ga ‘yan majalisar kasa daga kowacce jam’iyya da su goyi bayan dokar, ya kuma zargi kasashen yamma da tallata goyon baya ga ‘yancin masu auren jinsi a Senegal, da kuma jawo rudanin siyasa.


