AFCON 2025: Super Eagles Za Ta Fuskanci Babban Tara Saboda Sabbin Dokokin CAF.
Super Eagles na Najeriya da wasu kasashe da dama da suke cikin Gasar cin Kofin kasashen Afirka na 2025 da za’ayi a Morocco suna fuskantar babban tara bayan da Hukumar kwallon kafa ta Afirka (CAF) ta bayyana sabbin dokokin Gasar.

Kodayake Najeriya ta fitar da tawagar ‘Yan wasa 55 na wucin gadi don tun karar Gasar, CAF ta umarci duk kasashe su gabatar da jerin sunayen’Yan wasa na karshe kimanin kwanaki 10 kafin wasan farko.
Duk kasar da ta kasance ta kasa za’a ci tarar ta Dala 10,000.
CAF ta kuma gabatar da wasu karin ka’idoji don zurga-zurgan kungiyoyin da Shirye-shiryen wasan a duk lokacin Gasar:
CAF tace ‘Yan Wasa 18 ne kawai daga kowace Tawaga za’a ba su damar yin tafiya tsakanin Birane don wasanni, ko ta Jirgin sama, ko ta hanyar hanya ko kuma a Jirgin Kasa.
Dole ne ƙungiyoyin da ke tafiya daga Rabat zuwa Casablanca zasu yi hakan da safiyar wasan, yayin da waɗanda ke kan hanyarsu ta zuwa wasu biranen da za su karbi bakuncin gasar za su iya tafiya kwana ɗaya kafin wasanninsu.
Ƙasashen da ake sa ran za su yi tafiya a matakin rukuni sun haɗa da Zimbabwe, Afirka ta Kudu, Angola, Tanzania, Tunisia, Uganda, Botswana, Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo, Benin, Mozambique, Kamaru, Gabon, Comoros, Mali, Zambia, Sudan, Burkina Faso da Equatorial Guinea.
Ba za’a bar ƙungiyoyi su yi cikakken atisaye a wuraren da za’ayi wasa a jajibirin wasannin ba.
Madadin haka, za su iya ziyartar filin wasa ne kawai don sanin filin wasa tsakanin ƙarfe 2 na rana zuwa 9 na dare, bayan amincewar CAF kafin lokacin.
An tsara sabbin ƙa’idojin ne don sauƙaƙe dabaru da kuma tabbatar da daidaito a shirye-shiryen ƙungiyar yayin da Morocco ke karɓar baƙuncin babban wasan ƙwallon ƙafa na Afirka.
Da yake Gasar Cin Kofin kasashen Afirka AFCON 2025, na kara karatowa ana sa ran ƙungiyoyin ƙasa za su daidaita da canje-canjen da sauri ko kuma su fuskanci hukunci na tarar kuɗi.


