Tsohon kocin Super Eagles kuma kyaftin Sunday Oliseh ya ba Eric Chelle shawara mai muhimmanci.
Tsohon dan wasan Super Eagles Sunday Oliseh ya bukaci Eric Chelle da ya zamo mai tsauri da kuma kin amincewa da sa baki wajen yanke shawara kan fidda sunayen ‘yan Wasa na AFCON.
Duk da fargabar da Oliseh ke da ita game da nadin Chelle, domin ya fi son a bai wa dan Najeriya aikin maimakon wani dan Afirka, zakaran AFCON na 1994 ya yaba da kokarin da Chelle, ya yi zuwa yanzu.
Oliseh ya bayyana kwarin gwiwarsa, yana mai imanin cewa Super Eagles za su iya kaiwa dukkanin mataki a gasar cin kofin kasashen Afirka da za’ayi a Morocco.
Duk da haka, tsohon dan wasan tsakiya na Ajax ya dage cewa Chelle dole ne ya kasance mai dogewa akan abunda ya sani.
“Na san halin mutane , ina da kwarin gwiwa cewa Super Eagles za su iya yin abin da ya dace a wannan gasar,” in ji Oliseh.
“Abu na farko da nake ganin ya kamata manaja ya yi shi ne ya ɗan yi tsauri. Dole ne ya zama mai taurin kai domin ba wani abune a boye ba cewa mutane daga waje za su yi ƙoƙarin sanya bakin su kan wanda zaiyi wasa da wanda ba zaiyi ba.
“Ina ganin dole ya tsaya tsayin daka don nuna halinsa. Shi ne ke da alhakin ƙungiyar da kuma yanke shawara kan wanda zai yi wasa.”


