Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da kama Muhuyi Magaji Rimingado, wanda shine tsohon shugaban hukumar yaƙi da cin hanci ta jihar ranar Juma’a, inda ta yi zargi wasu ‘yan siyasa da hannu game da kamun nasa.
A sanarwar da ofishin Kwamashinan Shari’a Abdulkarim Maude ta ce jami’an ‘yansanda ne suka kama lauyan a ofishinsa da ke kan titin Zariya da misalin ƙarfe 5:30 na yamma, kuma suka tafi da shi hedikwatarsu da ke Bompai.
Antoni janar din ya bayyana kamen da “abin damuwa sosai” wanda “ya yi kama da yanayin aikin soja”. Ya yi iƙirarin cewa dakaru kusan 40 ne ɗauke da makamai suka je kama Muhuyi.
“Kwamashinan ya nuna cewa akwai yiwuwar lamarin yana da alaƙa da binciken da ake yi wa wasu manyan ‘yansiyasa, a jihar
Abdulkarim Maude ya kuma yi kira ga rundunar ‘yan sandan Najeriya ta yi cikakken bayani game da dalilin kama Muhuyi



