Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Published: December 8, 2025 at 10:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 8, 2025

Gwamnatin jihar Adamawa ta ayyana dokar hana fita na sa’o’i 24 a karamar hukumar Lamurde, sakamakon sake barkewar rikici a yankin.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan jihar Hussaini Hammangabdo, ya fitar a ranar Lahadi ta bayyana cewa an dauki matakin ne bayan sake tashin wata takaddama tsakanin al’ummomin yankin da yammacin ranar Lahadi.

A makon da ya gabata, al’ummomin Bachama da Chobo na karamar hukumar Lamurde sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a dakin taro na Banquet Hall da ke fadar Gwamnati a Yola.

Taron ya hadu da Hama Bachama, Homun Daniel Ismaila, manyan jiga igan al’umma, jami’an gwamnati da hukumomin tsaro.

Sanarwar ta kara da cewa: “Tuni an umurci hukumomin tsaro da su dauki matakan gaggawa domin dawo da zaman lafiya da doka a yankin.”

Gwamnati ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da nuna da hadin kai domin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s
Next Post: Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma

Karin Labarai Masu Alaka

Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi Labarai
  • Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.