Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin
Published: December 9, 2025 at 3:25 AM | By: Ibrahim Alfah Ahmad

Hukumomin Jamhuriyar Benin, sun fada jiya litinin cewa hare-haren da jiragen saman yaki na Najeriya suka kai sune suka gurgunta yunkurin juyin mulki a kasar, inda sojoji masu bore suka yi kokarin kama shugaba Patrice Talon.

Sojoji masu yunkurin juyin mulkin sun samu isa dab da Shugaba Talon, wanda ya gane ma idanunsa ba-ta-kashi tsakaninsu da masu gadinsa, kuma har sun iya suka kama wasu manyan hafsoshin soja guda biyu wadanda ba a sako su ba sai jiya litinin da safe.

Wadannan bayanan suna kumshe a cikin wata sanarwar da gwamnatin Jamhiriyar Benin ta wallafa game da yunkurin juyin mulkin, a bayan wani zaman majalisar ministocinta.

Sanarwar ta ce jiragen saman yakin Najeriya sun kai hare-hare suka lalata motocin yaki masu sulke na sojoji masu juyin mulkin, ba tare da sun kashe wani ba. Daga bisani, wasu zaratan sojoji daga kasar Cote D’Ivoire sun isa Cotonou, inda aka girka su domin daukar mataki ko da boren sojojin zai ci gaba.

Sojojin da suka yi yunkurin juyin mulkin sun fito daga sansanin soja na Togbin, inda tun kafin ketowar alfijir na ranar lahadi suka fara yada zango a gidan babban hafsan sojojin kasar, Janar Bertin Bada. An kashe matar janar din a gwabzawar da aka yi a wurin, amma hafsan ya samu ya tsere musu.

Sojojin sun samu suka kama babban hafsan sojojin kasa, Janar Abou Issa da Kanar Faizou Gomina, wadanda gwamnatin Benin ta ce an sako su daga bisani jiya litinin da safe a garin Tchaourou na arewacin kasar.

Masu yunkurin juyin mulkin, sun je suka kwace gidan telebijin na wani dan lokaci kafin a kore su, inda suka koma barikin Togbin, inda sojoji masu biyayya ga gwamnati da kuma jiragen saman yakin Najeriya suka yi ta far musu.

Har yanzu babu labarin inda Kanar Tigri Pascal yake, watau mutumin da aka ce shine jagoran masu yunkurin juyin mulkin.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio
Next Post: Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.