Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC
Published: December 9, 2025 at 5:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 9, 2025

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya,

Gwamna Fubara dai ya sanar da sauya sheƙar ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki a gidan gwamnati da ke birnin fatakwal na jihar Rivers.

Wannan dai na zuwa ne ƙasa da mako guda bayan da ƴan majalisar jihar 15 tare da kakakin majalisar suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ta APC.

Masu fashin baƙi dai na ganin sauya sheƙar ta Fubara ba lallai ta yi wa ministan Abuja, Nyesom Wike daɗi ba kasancewar shi ne babban abokin hamayyarsa, inda rikici ya kai har shugaba Tinubu ya saka wa jihar dokar ta-ɓaci ta watanni shida da ta tilasta Fubara sauka da kujerar gwamnan na tsawon watannin.

A watan Satumbar da ya gabata ne Fubara ya koma bakin aikinsa bayan ƙarewar wa’adin watannin shida na dokar ta ta-ɓacin da ta fara aiki a watan Maris a jihar sa.

Bisa tsarin siyasa, gwamnan jiha shi ne jagoran jam’iyya inda yanzu haka Fubara zai kasance jagoran jam’iyyar APC a jihar Rivers.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Next Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Zinari Yayi Tashin Gwauron Zabi Amurka
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.