Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC
Published: December 9, 2025 at 5:19 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 9, 2025

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya,

Gwamna Fubara dai ya sanar da sauya sheƙar ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki a gidan gwamnati da ke birnin fatakwal na jihar Rivers.

Wannan dai na zuwa ne ƙasa da mako guda bayan da ƴan majalisar jihar 15 tare da kakakin majalisar suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar ta APC.

Masu fashin baƙi dai na ganin sauya sheƙar ta Fubara ba lallai ta yi wa ministan Abuja, Nyesom Wike daɗi ba kasancewar shi ne babban abokin hamayyarsa, inda rikici ya kai har shugaba Tinubu ya saka wa jihar dokar ta-ɓaci ta watanni shida da ta tilasta Fubara sauka da kujerar gwamnan na tsawon watannin.

A watan Satumbar da ya gabata ne Fubara ya koma bakin aikinsa bayan ƙarewar wa’adin watannin shida na dokar ta ta-ɓacin da ta fara aiki a watan Maris a jihar sa.

Bisa tsarin siyasa, gwamnan jiha shi ne jagoran jam’iyya inda yanzu haka Fubara zai kasance jagoran jam’iyyar APC a jihar Rivers.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Next Post: Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Gwamnatin Kasar Benin Ta Nemi ‘Yan Kasa Su Kwantar Da Hankali Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Yau Litinin Za’a Mika Daliban Ga Iyayen Su Labarai
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.