Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC
Published: December 10, 2025 at 4:54 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya ce barin jam’iyyar PDP da ya yi ya biyo bayan gazawar jam’iyyar wajen kare shi a rikicin siyasar jihar.

Fubara, wanda ya bayyana haka a taron masu ruwa da tsaki a Fadar Gwamnati da ke Fatakwal, ya ce ganawarsa da Shugaba Bola Tinubu ta tabbatar masa da cikakken goyon bayan da PDP ta kasa bashi.

Ya kuma tabbatar da komawarsa jam’iyyar APC tare da manyan magoya bayansa, yana mai cewa jam’iyyar ta ba shi kariya da goyon bayan da ake buƙata domin tsallake rikicin siyasar Rivers.

“Da ba don Shugaba Tinubu ya shiga tsakani ba, da babu Siminalayi Fubara a yau,” in ji shi, yana mai bayyana kudurinsu na mara wa Tinubu baya a tazarcen 2027.

  • Sauya sheƙar Fubara yana ƙara sauya yanayin siyasar Rivers, tare da yiwuwar yin tasiri a zabukan 2027 masu zuwa.
Siyasa

Post navigation

Previous Post: Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa
Next Post: Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade

Karin Labarai Masu Alaka

Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Nanata Aniyar Mallakar Greeland Daga Kasar Denmark Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.