Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji
Published: December 10, 2025 at 10:53 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon shugaban Hukumar Karɓar Korafe-korafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya zargi tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, da hannu a kama shi da jami’an rundunar ‘yansandan Najeriya tayi a ranar Juma’a.

An kama Magaji ne a ofishinsa da ke Kano ta hannun wasu jami’an ‘yan sanda inda suka shaida masa cewa suna aiki ne da umarnin Sufeto Janar na ‘Yansanda.

Da yake zantawa da Manema labarai jim kaɗan bayan sakin sa a ranar Asabar, tsohon shugaban PCACC ya ce matsalarsa ta samo asali ne daga wasu korafe korafe da Ganduje da tsohon Manajan Daraktan Hukumar KASCO ta Jihar Kano, Bala Inuwa, suka shigar.

A cewarsa, Ganduje ya zarge shi da “ batanci” da suka shafi takaddamar shari’a da ake yi kan mallakar hannun jarin Gwamnatin Jihar Kano a kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

“Kun sani, tun da na bar kujerar shugaban PCACC, na koma aikin lauya gaba ɗaya, kuma ni ne babban lauya a shari’ar Dala Inland Dry Port,” in ji shi.

Ya bayyana cewa bayan kama shi, kai tsaye aka wuce da shi Abuja cikin tsauraran matakan tsaro.

“An kama ni, an tsare ni tsakanin jami’an ‘yan sanda zuwa Abuja, jami’ai biyu dauke da bindigogi a gefena, sannan wasu uku a kujerar gaba, aka tashi da ni daga Kano zuwa Abuja.

“Muka yi tafiya cikin dare har muka isa wajen ƙarfe 3:00 na asuba,” in ji shi.

Muhyi Magaji ya ƙara da cewa duk da ya dage yana neman a nuna masa takardar kama shi, jami’an sun ƙi nuna masa, suna cewa a Abuja za a gabatar masa.

Ya bayyana cewa an bayar da belinsa, sai dai an umarce shi da ya koma Abuja ranar Laraba tare da mika fasfon sa na fita ƙasashen waje.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade
Next Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami

Karin Labarai Masu Alaka

CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
Hukumar NAHCON Ta Bude Asibiti A Madina Afrika
Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.