Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika

Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu
Published: December 10, 2025 at 4:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Farfesa Wole Soyinka ya yi gargaɗi ga Shugaba Bola Tinubu kan yadda ake gudanar da tsaro da kuma amfani da jami’an gwamnati wajen kare wasu ‘yan tsiraru masu kusanci da fada.

Yayin bikin bayar da kyaututtuka na Wole Soyinka Centre for Investigative Journalism a Legas, a wani bidiyo da ya yadu, Soyinka ya ce ya yi mamakin ganin “babbar rundunar tsaro” da aka bai wa Seyi Tinubu, ɗan shugaban ƙasa, a Ikoyi.

Ya bayyana cewa yawan jami’an tsaron da ya gani “ya isa ya mamaye ƙaramar ƙasa,” lamarin da ya sa ya tuntubi mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin neman bayani.

Soyinka ya ce bai dace ‘ya’yan shugabanni su gaji karfin gwamnati ko su yi yawo da tsaro fiye da kima ba, yayin da ƙasar ke fama da hare-hare, garkuwa da mutane da rashin tsaro a sassa da dama.

Ya ƙara da cewa irin wadannan albarkatun tsaro ya fi dacewa a tura su wuraren da ake bukata, ba wajen kare masu gata ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci

Karin Labarai Masu Alaka

An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
  • An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya
  • Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.