Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan
Published: December 11, 2025 at 9:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe wasu mutane da dama a harin da aka kai da maraicen talata da jirgin saman drone a kusa da matatar mai mafi girma a kasar Sudan.

Rundunar sojojin wucin gadi ta RSF, wadda tun shekarar 2023 take gwabza yaki da rundunar sojojin kasar ta Sudan, ta ce sojojin gwamnati ne suka kai hari kan matatar dake Heglig, kwana guda a bayan da dakarun RSF suka kwace wannan matata dake kusa da bakin iyakar kasar da Sudan ta Kudu.

Dukkan sassan biyu sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa ba su da cikakken adadin wadanda aka kashe ko aka ji ma rauni, amma kafofin labarai a yankin sun ce an kashe shugabanni 7 na wasu kabilu tare da sojojin rundunar RSF

Rundunar RSF ta kuma ce akwai sojojin Sudan ta Kudu a wannan harin da ta ce ya saba dokoki na kasa da kasa.

Rundunar sojojin Sudan ta tabbatar da kai hari da jiragen drone wadanda ta ce an auna su ne a kan mayakan rundunar RSF.

Gwamnatin jihar Unity ta Sudan ta Kudu ta tabbatar da kashe sojoji uku na Sudan ta Kudu.

Afrika

Post navigation

Previous Post: NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas
Next Post: Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Ma’aikacin VOA Saleh Shehu Ashaka Ya Rasu Afrika
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.