Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro
Published: December 14, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa rundunar kar-ta-kwana domin ƙarfafa tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a faɗin jihar.

Wannan na cikin sanarwar da Daraktan Yada Labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi 14 ga Disamba 2025.

Sanarwar ta ce an ɗauki matakin ne domin dakile shigowar masu aikata laifuka, musamman a wuraren da ake yawan zirga-zirga, ciki har da tashoshin mota da wuraren shigowa da fita daga birnin Kano.

Rundunar kar-ta-kwanan za ta riƙa sa ido, tattara bayanan sirri da aiwatar da ayyukan tsaro tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sanarwar ta ƙara da cewa aikin rundunar zai shafi har da gidajen mai da sauran wuraren taruwar jama’a da ake ganin zai iya haifar da barazanar tsaro.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro
Next Post: Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tarkacen Makamai Masu Linzami Sun Lalata Gidaje Da Wuraren Kasuwancin Palasdinawa Afrika
Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
  • Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.