Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro
Published: December 14, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kafa rundunar kar-ta-kwana domin ƙarfafa tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a faɗin jihar.

Wannan na cikin sanarwar da Daraktan Yada Labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi 14 ga Disamba 2025.

Sanarwar ta ce an ɗauki matakin ne domin dakile shigowar masu aikata laifuka, musamman a wuraren da ake yawan zirga-zirga, ciki har da tashoshin mota da wuraren shigowa da fita daga birnin Kano.

Rundunar kar-ta-kwanan za ta riƙa sa ido, tattara bayanan sirri da aiwatar da ayyukan tsaro tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sanarwar ta ƙara da cewa aikin rundunar zai shafi har da gidajen mai da sauran wuraren taruwar jama’a da ake ganin zai iya haifar da barazanar tsaro.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro
Next Post: Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau

Karin Labarai Masu Alaka

Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.