Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Published: December 15, 2025 at 6:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ko CDEAO, ta bayyana rashi yardarta da shirin mayar da mulki hannun farar hula da shugabannin mulkin soja na Guinea-Bissau, suka bayyana, tana mai bukatar da a gaggauta maido da aiki da tsarin mulki.

Shugabannin ECOWAS, sun yi barazanar saka takunkumi na musamman a kan duk wadanda ke kawo cikas ga maido da mulkin farar hula a kasar.

A ranar 26 ga watan Nuwamba ne wasu hafsoshin soja a Guinea-Bissau suka hambarar da shugaba Umaro Sissoco Embalo, kwana daya kafin a bayyana sakamakon zaben shugaban kasa, kashegari kuma suka ayyana Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban gwamnatin mulkin soja na wuin gadi.

Wannan juyin mulki da aka yi a Gyuinea-Bissau, shine na tara cikin shekaru 5 da suka shige a yankin yammaci da tsakiyar Afirka, abinda ya kara irin fargabar da ake yi ta zaizayewar mulkin dimokuradiyya a wannan yanki mai fama da rashin tsaro da rashin kwanciyar hankalin siyasa.

Shugabannin dake halartar taron kolin shekara na kungiyar ECOWAS ranar lahadi a Abuja, babban birnin Najeriya, sun yi kiran da a sako dukkan ‘yan siyasar da aka kama, ciki har da shugabannin hamayya, a kuma tsara shirin maida mulki cikin gaggawa wanda zai kumshi dukkan sassan kasar cikin gaggawa.

Shugaban majalisar zartasa ta kungiyar ECOWAS, Omar Touray, yace matakin da shugabannin kungiyar suka dauka shine na tabbatar da cewa sam ba za a taba yarda da sauya gwamnati ta hanyar da tsarin mulki bai amince ba.

ECOWAS ta ce ‘yan kallonta, da na Kungiyar Tarayyar Afirka da na kasashe masu magana da harshen Portugal duk sun ce zaben shugaban kasa da aka gudanar a Guinea-Bissau, an yi shi cikin adalci.

Har ila yau kungiyar ta umurci shugabanta da ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’ai zuwa Gyuinea-Bissau domin tattaunawa da hukumomin sojan kasar.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
  • Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
  • Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni
  • Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
  • Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.