Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Published: December 15, 2025 at 6:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ko CDEAO, ta bayyana rashi yardarta da shirin mayar da mulki hannun farar hula da shugabannin mulkin soja na Guinea-Bissau, suka bayyana, tana mai bukatar da a gaggauta maido da aiki da tsarin mulki.

Shugabannin ECOWAS, sun yi barazanar saka takunkumi na musamman a kan duk wadanda ke kawo cikas ga maido da mulkin farar hula a kasar.

A ranar 26 ga watan Nuwamba ne wasu hafsoshin soja a Guinea-Bissau suka hambarar da shugaba Umaro Sissoco Embalo, kwana daya kafin a bayyana sakamakon zaben shugaban kasa, kashegari kuma suka ayyana Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban gwamnatin mulkin soja na wuin gadi.

Wannan juyin mulki da aka yi a Gyuinea-Bissau, shine na tara cikin shekaru 5 da suka shige a yankin yammaci da tsakiyar Afirka, abinda ya kara irin fargabar da ake yi ta zaizayewar mulkin dimokuradiyya a wannan yanki mai fama da rashin tsaro da rashin kwanciyar hankalin siyasa.

Shugabannin dake halartar taron kolin shekara na kungiyar ECOWAS ranar lahadi a Abuja, babban birnin Najeriya, sun yi kiran da a sako dukkan ‘yan siyasar da aka kama, ciki har da shugabannin hamayya, a kuma tsara shirin maida mulki cikin gaggawa wanda zai kumshi dukkan sassan kasar cikin gaggawa.

Shugaban majalisar zartasa ta kungiyar ECOWAS, Omar Touray, yace matakin da shugabannin kungiyar suka dauka shine na tabbatar da cewa sam ba za a taba yarda da sauya gwamnati ta hanyar da tsarin mulki bai amince ba.

ECOWAS ta ce ‘yan kallonta, da na Kungiyar Tarayyar Afirka da na kasashe masu magana da harshen Portugal duk sun ce zaben shugaban kasa da aka gudanar a Guinea-Bissau, an yi shi cikin adalci.

Har ila yau kungiyar ta umurci shugabanta da ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’ai zuwa Gyuinea-Bissau domin tattaunawa da hukumomin sojan kasar.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya

Karin Labarai Masu Alaka

Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
  • Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.