Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Published: December 15, 2025 at 8:55 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu kwararru kan harkokin tsaro a Amurka sun ce tayin da kasar Ukraine ta yi na yin watsi da burin neman shiga cikin kungiyar kawancen tsaro ta NATO, bai kai wanda zai iya canja akalar tattaunawar neman sulhun da ake yi yanzu ba.

A lokacin tattaunawa da wakilan Amurka ranar lahadi a kan shirin sulhu tsakanin Rasha da Ukraine, shugaba Volodymyr Zeklensky yayi tayin watsar da yunkurin da kasarsa ke yi na neman shiga kungiyar kawancen tsaro ta NATO.

Shugaban yace maimakon neman shiga NATO, kasar zata nemi tabbacin na tsaro, watau kariya daga Amurka da kasashen Turai da wasunsu.

Daraktan nazarin tsaro da manufofin hulda da kasashen waje cibiyar nan ta CATO institute, Justin Logan, yace wannan tayin ba zai canja komai a tattaunawar neman sulhun da ake yi ba, yana mai fadin cewa wannan wani yunkuri ne kawai da Ukraine keyi na neman nuna cewa tana son a yi sulhu.

Logan da wani farfesa na nazarin muhimman muradu na kasa a Jami’ar Florida, Andrew Michta, sun ce da ma zai yi wuya ga Ukraine ta samu shiga kungiyar ta NATO, saboda haka wannan ba wani muhimmin batu ba ne a yanzu.

Sai dai kuma, ba kowa ne yayi watsi da tayin na Zelensky ba amma wani tsohon mai bada shawara kan hulda da kasashen waje a gwamnatin shugaba Obama , Brett Bruen, yace wannan sassauci da Ukraine ta yi babba ne kuma yana da muhimmanci, domin kuwa Zelensky yana nuna ma duniya cewa shi mai neman zaman lafiya ne، yayin da har yanzu babu wani abu guda da kasar Rasha ta nuna sassauci a kai daga cikin bukatunta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa
Next Post: Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Afrika
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
  • Osun: Adeleke Ya Doke Oyebamiji, Ya Ci Gaba Da Rike Kujerar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.