Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO
Published: December 15, 2025 at 8:55 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wasu kwararru kan harkokin tsaro a Amurka sun ce tayin da kasar Ukraine ta yi na yin watsi da burin neman shiga cikin kungiyar kawancen tsaro ta NATO, bai kai wanda zai iya canja akalar tattaunawar neman sulhun da ake yi yanzu ba.

A lokacin tattaunawa da wakilan Amurka ranar lahadi a kan shirin sulhu tsakanin Rasha da Ukraine, shugaba Volodymyr Zeklensky yayi tayin watsar da yunkurin da kasarsa ke yi na neman shiga kungiyar kawancen tsaro ta NATO.

Shugaban yace maimakon neman shiga NATO, kasar zata nemi tabbacin na tsaro, watau kariya daga Amurka da kasashen Turai da wasunsu.

Daraktan nazarin tsaro da manufofin hulda da kasashen waje cibiyar nan ta CATO institute, Justin Logan, yace wannan tayin ba zai canja komai a tattaunawar neman sulhun da ake yi ba, yana mai fadin cewa wannan wani yunkuri ne kawai da Ukraine keyi na neman nuna cewa tana son a yi sulhu.

Logan da wani farfesa na nazarin muhimman muradu na kasa a Jami’ar Florida, Andrew Michta, sun ce da ma zai yi wuya ga Ukraine ta samu shiga kungiyar ta NATO, saboda haka wannan ba wani muhimmin batu ba ne a yanzu.

Sai dai kuma, ba kowa ne yayi watsi da tayin na Zelensky ba amma wani tsohon mai bada shawara kan hulda da kasashen waje a gwamnatin shugaba Obama , Brett Bruen, yace wannan sassauci da Ukraine ta yi babba ne kuma yana da muhimmanci, domin kuwa Zelensky yana nuna ma duniya cewa shi mai neman zaman lafiya ne، yayin da har yanzu babu wani abu guda da kasar Rasha ta nuna sassauci a kai daga cikin bukatunta.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa
Next Post: Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Girke Jirage Marasa Matuki Tare Da Sojoji A Najeriya Afrika
Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
  • Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Kasar Congo Ta Dau Alwashin Bin Tsari Wajen Rarraba Ma’adanai Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.