Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu
Published: December 17, 2025 at 3:05 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Majalissar wakilai ta rikon kwaryar jamhuriyar Nijar ta fara zamanta na biyu na karshe a shekarar nan ta 2025.
A tsawon kwanaki biyu na wannan zama wakilan zasu tattauna batutuwa da dama da suka shafi tafiyar kasar kamar yadda  gwamnatin mulkin sojan kasar ta shigar da bukata. Sai dai wasu ‘yan kasar sun shawarci majalissar a kan wasu karin batutuwan da ke bukatar matakan gaggawa.
 Taron Wanda ke matsayin na rufe shekarar nan ta 2025 lokaci ne da wakilai 194 na majalissar ta conseil consultatif de la refondation zasu nazarci kudirorin da gwamnatin ta Nijar ta zo da su da suka shafi fannoni da dama.
Farfesa Dicko Abdourahamane na daga cikin mahalarta taron.
Kundin tsarin mulkin gwamnatin ta rikon kwarya da ya samo asali daga babban taron rukunonin al’ummar kasar ya bai wa majalissar hurumin sauraren mimbobin gwamnati idan bukatar hakan ta taso saboda haka a wannan karon za su mori wannan dama kamar yadda shugaban kwamitin kula da siyasar duniya a majalissar CCR Bana Ibrahim ya bayyana.
Duk da cewa zaman na da mahimmanci a wajensu wasu ‘yan Nijar kamar su Salissou Ibrahim na FRSA na jan hankula a kula da wasu abubuwan da a cewarsa suna kan gaba a jerin manufofin shugaban kasa.
Shi kuma shugaban kungiyar yaki da cin hanci ta RENAC kwararre kan sha”anin shugabanci Adamou Oumarou na kokarin ankarar da zaman na wannan karon kan matakan taka birki daga yunkurin ciyo bashi daga waje.
A karshen taron na kwanaki 15 majalissar ta CCR za ta gabatar da takardun shawarwari wa bangaren zartarwa inda Janar Abdourahamane Tiani da ke da maganar karshe zai yi na’am kokuma ya bukaci majalissar ta yi Zaman gaggawa don kwaskware abinda ke bukatar gyara.
TARON MAJALISSAR WAKILAI
Afrika

Post navigation

Previous Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Next Post: Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika
Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.