Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum
Published: December 17, 2025 at 11:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Yobe a arewa maso gabashin Najeriya ta tabbatar da samuwar wata ƙungiyar dake lalata tare da cin zarafin fursunoni a Gidan Gyaran Hali na Potiskum.

Mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Abdulsalam Abubakar mai ritaya, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron Majalisar Tsaron Jihar da aka gudanar a ranar Talata a Damaturu.

Abdulsalam ya bayyana lamarin a matsayin babbar cin amana, inda ya ce ana zargin wasu jami’an gidan yari da yi wa wata fursuniya ciki a cikin gidan gyaran halin.

Ya ce hakan na nuna sakaci wajen aiki da kuma rashin kulawa yadda ya kamata, yana mai cewa a ka’ida babu yadda za a yi jami’in tsaro namiji ya shiga sashen mata idan ana sa ido yadda ya dace.

Mai ba da shawarar kan tsaro ya ce, bincike na ci gaba da gudana, inda ya kara da cewa har yanzu ba a tantance adadin jami’an da ke da hannu a lamarin ba, domin ana ci gaba da kama wasu da ake zargi inda ya kara da cewa, al’amarin wata ƙungiya ce mai faɗi, bawai mutum ɗaya ba, kuma akwai masu taimaka musu ciki har da wasu jami’an mata.

Sai dai Abdulsalam ya nuna fatan cewa duk wanda aka samu da laifi a binciken da Hedikwatar Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa ke gudanarwa, za a miƙa shi ga ‘yan sanda domin gurfanar da shi a gaban kotu.

Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta riga ta kai ƙorafi ga shugabancin Hukumar Gyaran Hali ta Ƙasa da Ma’aikatar Harkokin Cikin gida yana mai jaddada cewa gwamnati na da alhakin kare rayuka, dukiya da mutuncin al’umma.

A game da samar da tsaro lokacin bukukuwan Kirsimeti, Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar, Emmanuel Ado, ya ce an shirya tsaro sosai, inda aka tura jami’ai da dama zuwa wuraren ibada da wuraren shakatawa.

Ya tabbatar wa mazauna jihar, musamman mabiya addinin Kirista, cewa za su gudanar da bukukuwansu cikin kwanciyar hankali ba tare da fargaba ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Next Post: Gwamnatin Gombe Zata Inganta Samar Da Wuta Wajen Amfani Da Hasken Rana

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Dakarun Pakistan Da Afghanistan Sunyi Arrangama Labarai
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
  • Majalisun Najeriya Sun Amince Ta Karin Kasafin Kudi Afrika
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.