Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya Afrika
  • Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya. Labarai

Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami
Published: December 17, 2025 at 9:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) ta rufe wani gida da ke da alaka da tsohon Antoni Janar na ƙasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, a daren Laraba, a matsayin wani bangare na binciken cin hanci da rashawa da ake yi masa.

Rahotanni sun ce jami’an EFCC tare da jami’an tsaro sun isa gidan, inda aka ce Nana Hadiza Buhari, ’yar tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari kuma matar Malami, tana nan a lokacin da aka gudanar da aikin.

Matakin na zuwa ne yayin da EFCC ke ci gaba da tsare Malami bisa zargin cin hanci da rashawa, halasta kudaden haram da wasu laifuka da suka shafi kudaden Abacha da aka kwato.

EFCC ta bayyana cewa belin da aka ba Malami a baya an soke shi saboda rashin cika sharudda, kuma har yanzu yana hannun hukuma domin ci gaba da bincike.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa daga bangaren Malami ko iyalan Buhari kan lamarin.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai
Next Post: ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato
  • Za’ayi Auren Zawarawa Dubu Uku A Kano
  • Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe
  • NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
  • Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Masar Ta Dakatar Da Wasu Ayyukan Da Ake Amfani Da Man Fetur Da Diesel Labarai
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.