Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11
Published: December 18, 2025 at 7:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Burkina Faso ta saki mayakan Najeriya su 11 wadanda ta tsare fiye da mako guda da ya shige, a bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya fada ranar alhamis cikin wata sanarwa ta kafar X cewa an warware batun matuka jirgin saman yakin Najeriya da mutanen dake cikin jirgin ta hanyar diflomasiyya.

Sanarwar ta ce gwamnatin mulkin soja ta Burkina Faso a karkashin jagorancin Ibrahim Traore, ta sako sojojin saman a bayan ganawa da wata tawagar Najeriya karkashin jagorancin Tuggar.

A makon da ya shige rundunar mayakan saman Najeriya ta ce jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Portugal domin sabis da aka saba yi ma jirage a lokacin da yayi saukar gaggawa a garin Bobo Dioulasso a yammacin Burkina.

Amma kuma gidan talabijin na kasar Burkina Faso ya watsa wani jawabin ministan harkokin wajen Najeriya Tuggar ranar laraba, inda yake cewa an bi ta hanyoyin da ba su dace ba wajen neman izinin wucewar jirgin ta samaniyar kasar, ya kuma nemi ahuwar hakan.

Shugaban gwamnatin mulkin soja ta kasar Mali, Janar Assimi Goita, ya ce saukar gaggawar da jirgin na Najeriya yayi, ya sa Kungiyar Kasashen Yankin Sahel ta sanya dakarun tsaron samaniyarta cikin shirin ko ta kwana, tare da ba su iznin harbo duk wani jirgin da ya shiga samaniyar yankin ba tare da izni ba.

Wannan kungiya ta kunshi kasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce a yanzu matuka jirgin saman zasu wuce da shi wurin gyara a kasar Portugal.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Next Post: Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
  • An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai
  • Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.