Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11
Published: December 18, 2025 at 7:17 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Burkina Faso ta saki mayakan Najeriya su 11 wadanda ta tsare fiye da mako guda da ya shige, a bayan da jirginsu yayi saukar gaggawa.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya fada ranar alhamis cikin wata sanarwa ta kafar X cewa an warware batun matuka jirgin saman yakin Najeriya da mutanen dake cikin jirgin ta hanyar diflomasiyya.

Sanarwar ta ce gwamnatin mulkin soja ta Burkina Faso a karkashin jagorancin Ibrahim Traore, ta sako sojojin saman a bayan ganawa da wata tawagar Najeriya karkashin jagorancin Tuggar.

A makon da ya shige rundunar mayakan saman Najeriya ta ce jirgin yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Portugal domin sabis da aka saba yi ma jirage a lokacin da yayi saukar gaggawa a garin Bobo Dioulasso a yammacin Burkina.

Amma kuma gidan talabijin na kasar Burkina Faso ya watsa wani jawabin ministan harkokin wajen Najeriya Tuggar ranar laraba, inda yake cewa an bi ta hanyoyin da ba su dace ba wajen neman izinin wucewar jirgin ta samaniyar kasar, ya kuma nemi ahuwar hakan.

Shugaban gwamnatin mulkin soja ta kasar Mali, Janar Assimi Goita, ya ce saukar gaggawar da jirgin na Najeriya yayi, ya sa Kungiyar Kasashen Yankin Sahel ta sanya dakarun tsaron samaniyarta cikin shirin ko ta kwana, tare da ba su iznin harbo duk wani jirgin da ya shiga samaniyar yankin ba tare da izni ba.

Wannan kungiya ta kunshi kasashen Mali, Burkina Faso da Jamhuriyar Nijar.

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta ce a yanzu matuka jirgin saman zasu wuce da shi wurin gyara a kasar Portugal.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Next Post: Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa

Karin Labarai Masu Alaka

Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.