Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia
Published: December 22, 2025 at 9:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministocin harkokin wajen Kungiyar Kasashen yankin Kudu Maso Gabashin Asiya, zasu gana yau litinin a kasar Malaysia, da zummar kawo karshen yakin bakin iyakar da ya kashe mutane akalla 40 tare da raba mutane fiye da rabin miliyan da gidajensu cikin wannan wata a tsakanin Thailand da Cambodia.

Ministocin zasu yi kokarin farfado da shirin tsagaita wutar da aka yi aiki da shi na dan kankanin lokaci, wanda Malaysia mai rike da kujerar shugabancin kungiyar da kuma shugaba Donald Trump na Amurka suka kulla a tsakanin kasashen biyu.

Kasashen Thailand da Cambodia, wadanda su ma membobin wannan kungiya ne da ake kira ASEAN a takaice, zasu halarci taron na yau a kuala Lumpur, wannan zai zamo ido hudu na farko da jami’an kasashen biyu zasu yi da juna tun sake barkewar fada a ranar 8 ga watan nan na Disamba.

A bayan wannan yunkuri da kasashen yankin ke yi, Amurka da kasar China su ma kowacce tana nata kokarin na ganin an samu zaman lafiya a bakin iyakar kasashen biyu, amma har yanzu babu wata alama ta wanzuwar zaman lafiya.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Next Post: Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
  • GTA Hausa Logo
    Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Anyi Jana’izar Mahaifiyar Nasiru El Rufai A Abuja Afrika
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.