Ministocin harkokin wajen Kungiyar Kasashen yankin Kudu Maso Gabashin Asiya, zasu gana yau litinin a kasar Malaysia, da zummar kawo karshen yakin bakin iyakar da ya kashe mutane akalla 40 tare da raba mutane fiye da rabin miliyan da gidajensu cikin wannan wata a tsakanin Thailand da Cambodia.
Ministocin zasu yi kokarin farfado da shirin tsagaita wutar da aka yi aiki da shi na dan kankanin lokaci, wanda Malaysia mai rike da kujerar shugabancin kungiyar da kuma shugaba Donald Trump na Amurka suka kulla a tsakanin kasashen biyu.
Kasashen Thailand da Cambodia, wadanda su ma membobin wannan kungiya ne da ake kira ASEAN a takaice, zasu halarci taron na yau a kuala Lumpur, wannan zai zamo ido hudu na farko da jami’an kasashen biyu zasu yi da juna tun sake barkewar fada a ranar 8 ga watan nan na Disamba.
A bayan wannan yunkuri da kasashen yankin ke yi, Amurka da kasar China su ma kowacce tana nata kokarin na ganin an samu zaman lafiya a bakin iyakar kasashen biyu, amma har yanzu babu wata alama ta wanzuwar zaman lafiya.


