Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila
Published: December 23, 2025 at 9:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da korar Adamu Abdullahi Danko da wasu mataimaka uku nan take bayan binciken cin zarafin da aka yiwa, Abdulrahman Abubakar Sheriff, Kansila mai wakiltar gundumar Shamaki a karamar hukumar Gombe.

Matakin wadda Sakataren Gwamnatin jihar Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi ya sanar, ya biyo bayan kafa kwamitin bincike na musamman ne kan lamarin.

Sakamakon binciken kwamitin wanda rahotannin hukumomin tsaro suka tabbatar ne ya kai ga matakin da Gwamnan ya ɗauka.

A cewar Sakataren Gwamnatin Jihar, masu taimakawa gwamnan da abin ya shafa sune, Adamu Abdullahi Danko – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Harkokin Cikin Gida, da Garba Mohammed Mai Rago – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan harkokin Siyasa, da Rabiu Sulaiman Abubakar – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Kafafen Sada Zumunta na Zamani da kuma Ali Ibrahim Baban Kaya – Babban Mataimaki na Musamman na 2 kan Hulɗa da al’umma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bada umarnin cewa korar ta fara aiki ne nan take.

An kuma umurci duk jami’an da abin ya shafa su miƙa duk kadarorin gwamnati dake hannunsu ga hukumomin da suka dace ba tare da wani ɓata lokaci ba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci tashin hankali, rashin ɗa’a da cin zarafi ba, yana mai cewa ba zai lamunci duk abinda zai iya yin barazana ga zaman lafiyar jama’a ko lalata amincin da gwamnatinsa ke da shi a idon al’ummar jihar ba.

Ya tabbatarwa al’ummar jihar Gombe jajircewar gwamnatinsa wajen tabbatar da bin doka da oda, riƙon amana da kuma zaman lafiya sannan ya ƙara da cewa za a ɗauki matakai masu tsauri don kare zaman lafiya da ɗorewar kwanciyar hankalin da jihar take ta fafutukar ɗabbaƙawa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar
Next Post: Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
  • Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.