Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar
Published: December 24, 2025 at 10:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikata a kasar Masar sun fara harhada wani tsohon jirgin ruwan kwale-kwale na wani fir’auna da ya mulki daular dubban shekaru da suka shige.

Ma’aikata sun fara harhada wannan kwale-kwale a bainar jama’a a sabon makeken dakin kayan tarihi na Masar ranar talata da safe, yayin da ‘yan yawon bude ido suka tsaya su na kallo.

Wannan kwale-kwale mai tsayin mita 42, na wani fir’auna ne, ko sarki, na masar mai suna Khufu, kuma shugaban sashen gyarawa da farfado da kayan tarihi Issa Zeidan yace zasu dauki shekaru hudu suna wannan aiki na sake hada wannan kwale-kwale baki dayansa, yace jirgin ya kunshi katako dai-dai har guda 1650.

Sarki Khufu ya mulki Daular Masar shekatu 4500 da suka shige, kuma shine ya gina babbar dalar nan ta Giza.

Minsitan yawon shakatawa da kula da kayayyakin tarihi na Masar, Sherif fathy, yace wannan aiki yana daya daga cikin ayyukan sake farfado da wani abu na tarihi mafi muhimmanci a wannan karni.

A watan da ya shige aka bude wannan gagarumin dakin ajiye kayayyakin tarihi na Masar wanda aka gina a kan kudi dala maitan dubu 1, inda kuma ake kokarin sake harhada wannan kwale-kwale, kuma aikin tarihin yana dauke da kayayyaki kusan dubu 50, cikinsu har da kayayyakin da aka samo daga cikin kabarin sanannen Fir’aunan nan mai suna Tutankhamun wanda aka gano a shekarar 1922.

Wannan kwale kwale da ake kokarin sake harhadawa yana daga cikin wasu guda biyu da aka gani a shekarar 1954 a gefen bangaren kudu na Dalar Giza, an fara tono shi daga inda yashi ya binne shi a shekarar 2014.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya
Next Post: Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami

Karin Labarai Masu Alaka

Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi Afrika
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya Najeriya
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
  • Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.