Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami
Published: December 24, 2025 at 11:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kotun FCT Abuja ta bayar da belin wucin gadi ga Abubakar Malami, ta dage sauraron shari’a zuwa 5 ga Janairu

Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke Abuja Najeriya ta bayar da belin wucin gadi ga tsohon Babban Lauyan kasar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, a shari’ar da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ke gabatarwa a kansa.

Mai shari’a Bello Kawu ne ya yanke wannan hukunci a ranar Talata, 23 ga Disamba, 2025, yayin sauraron ƙarar mai lamba M/17220/2025.

Kotun ta ce an bayar da belin ne bisa sharuddan da EFCC ta riga ta gindaya tun farko, waɗannan sun haɗa da mika fasfo ɗin tafiyar ƙasashen waje na Malami, tare da cike takardun beli daga mutane biyu masu tsaya masa.

Mutanen da za su tsaya masa su ne Daraktan Janar na Hukumar Tallafin Shari’a ta Ƙasa (Legal Aid Council) da kuma ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Augie/Argungu.

Mai shari’a Kawu ya kuma sake dubawa tare da farfaɗo da sharuɗɗan belin da aka riga aka cika tun 28 ga Nuwamba, 2025, ciki har da mika fasfo da kuma gabatar da mutanen da za su tsaya masa.

Kotun ta bayyana cewa an bayar da belin wucin gadin ne bisa dalilin tsananin wahala ta musamman, har zuwa lokacin da za a saurara kuma a yanke hukunci kan babbar ƙarar da ke gaban kotu.

An dage sauraron shari’ar zuwa 5 ga Wata Janairu, 2026, domin jin ƙarar a hukumance.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar
Next Post: Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027 Afrika
Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Nwakali Na Dab Da Komawa Kungiyar PAC Omonia Ta Cyprus Wasanni
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.